Aya :
1
وَٱلۡعَٰدِيَٰتِ ضَبۡحٗا
Ina rantsuwa da dawãki mãsu gudu suna fitar da kũkan ciki.
Aya :
2
فَٱلۡمُورِيَٰتِ قَدۡحٗا
Mãsu ƙyasta wuta (da kõfatansu a kan duwatsu) ƙyastawa.
Aya :
3
فَٱلۡمُغِيرَٰتِ صُبۡحٗا
Sa'an nan mãsu yin hari a lokacin asuba.
Aya :
4
فَأَثَرۡنَ بِهِۦ نَقۡعٗا
Sai su motsar da ƙũra game da shi.
Aya :
5
فَوَسَطۡنَ بِهِۦ جَمۡعًا
Sai su shiga, game da ita (ƙũrar), a tsakãnin jama'ar maƙiya.
Aya :
6
إِنَّ ٱلۡإِنسَٰنَ لِرَبِّهِۦ لَكَنُودٞ
Lalle ne mutum mai tsananin butulci ne ga Ubangijinsa.
Aya :
7
وَإِنَّهُۥ عَلَىٰ ذَٰلِكَ لَشَهِيدٞ
Lalle ne shi mai shaida ne a kan laifinsa da haka.
Aya :
8
وَإِنَّهُۥ لِحُبِّ ٱلۡخَيۡرِ لَشَدِيدٌ
Kuma alle ne ga dũkiya shi mai tsananin so ne.
Aya :
9
۞ أَفَلَا يَعۡلَمُ إِذَا بُعۡثِرَ مَا فِي ٱلۡقُبُورِ
Shin, bã ya da sanin lõkacin da aka tõne abin da yake cikin kaburbura.