Fassarar Ma'anonin Alqura'ni

Hausa language - Abu Bakr Jomy

Scan the qr code to link to this page

سورة الفيل

Lambar shafi

Aya

Bude Nassin Ayar
Bude Rataye
Share this page

Aya : 1
أَلَمۡ تَرَ كَيۡفَ فَعَلَ رَبُّكَ بِأَصۡحَٰبِ ٱلۡفِيلِ
Ashe, ba ka ga yadda Ubangijin ka Ya aikata ga mutanen giwa* ba?
* An yi Yãƙin Gĩwa shekarar haihuwar Annabi tsakãnin halaka su da haihuwarsa kwãna hamsin. Bayan shekara arba'in Annabi ya fara karantar da mutane. Ya karantar da su cikin shekara ashirin da uku, sa'an nan ya ƙaura. Bayansa da shekara hamsin waanda suka bi shi suka cinye duniya. Wannan yana nuna cewa mutane ba su samun daraja sai da riƙon addini da ilimi.
Aya : 2
أَلَمۡ يَجۡعَلۡ كَيۡدَهُمۡ فِي تَضۡلِيلٖ
Ashe, bai sanya kaidin su a cikin ɓata ba?
Aya : 3
وَأَرۡسَلَ عَلَيۡهِمۡ طَيۡرًا أَبَابِيلَ
Kuma Ya sako, a kansu, wasu tsuntsãye, jama'a-jama'a.
Aya : 4
تَرۡمِيهِم بِحِجَارَةٖ مِّن سِجِّيلٖ
Suna jifar su da wasu duwatsu na yumɓun wuta.
Aya : 5
فَجَعَلَهُمۡ كَعَصۡفٖ مَّأۡكُولِۭ
Sa'an nan Ya sanya su kamar karmami wanda aka cinye?
An aika shi cikin Nasara