Fassarar Ma'anonin Alqura'ni

Hausa language - Abu Bakr Jomy

Scan the qr code to link to this page

سورة النازعات

Lambar shafi

Aya

Bude Nassin Ayar
Bude Rataye
Share this page

Aya : 1
وَٱلنَّٰزِعَٰتِ غَرۡقٗا
Ina rantsuwa da mala'iku mãsu fisgar rãyuka (na kafirai) da ƙarfi.
Aya : 2
وَٱلنَّٰشِطَٰتِ نَشۡطٗا
Da mãsu ɗibar rãyuka (na mũminai) da sauƙi a cikin nishãɗi.
Aya : 3
وَٱلسَّٰبِحَٰتِ سَبۡحٗا
Da mãsu sauka daga sama da umurnin Allah kamar suna iyo.
Aya : 4
فَٱلسَّٰبِقَٰتِ سَبۡقٗا
Sa'an nan, su zama mãsu gaugãwa (da umarnin Allah) kamar suna tsẽre.
Aya : 5
فَٱلۡمُدَبِّرَٰتِ أَمۡرٗا
Sa, an nan, su kasance masu shirya gudanar da umarni.
Aya : 6
يَوۡمَ تَرۡجُفُ ٱلرَّاجِفَةُ
Rãnar da mai girgiza abũbuwa (bũsar farko) zã ta kaɗa.
Aya : 7
تَتۡبَعُهَا ٱلرَّادِفَةُ
Mai biyar ta (bũsa ta biyu) nã biye.
Aya : 8
قُلُوبٞ يَوۡمَئِذٖ وَاجِفَةٌ
Wasu zukãta, a rãnar nan, mãsu jin tsõro ne.
Aya : 9
أَبۡصَٰرُهَا خَٰشِعَةٞ
Alhãli idãnunsu na ƙasƙantattu.
Aya : 10
يَقُولُونَ أَءِنَّا لَمَرۡدُودُونَ فِي ٱلۡحَافِرَةِ
Sunã cẽwa "Ashe lalle zã a iya mayar da mu a kan sãwunmu?
Aya : 11
أَءِذَا كُنَّا عِظَٰمٗا نَّخِرَةٗ
"Ashe, idan muka zama ƙasusuwa rududdugaggu?"
Aya : 12
قَالُواْ تِلۡكَ إِذٗا كَرَّةٌ خَاسِرَةٞ
Suka ce: "Waccan kam kõmãwa ce, tãɓaɓɓiya!"
Aya : 13
فَإِنَّمَا هِيَ زَجۡرَةٞ وَٰحِدَةٞ
To, ita kam, tsãwa guda kawai ce.
Aya : 14
فَإِذَا هُم بِٱلسَّاهِرَةِ
Sai kawai gã su a bãyan ƙasa.
Aya : 15
هَلۡ أَتَىٰكَ حَدِيثُ مُوسَىٰٓ
Shin, lãbãrin Mũsã ya zo maka?

Aya : 16
إِذۡ نَادَىٰهُ رَبُّهُۥ بِٱلۡوَادِ ٱلۡمُقَدَّسِ طُوًى
A lõkacin da Ubangijinsa Ya kirãye shi, a cikin kwari mai tsarki, wato Duwã?
Aya : 17
ٱذۡهَبۡ إِلَىٰ فِرۡعَوۡنَ إِنَّهُۥ طَغَىٰ
Ka tafi zuwa ga Fir'auna, lalle ne shi, ya ƙẽtare haddi.
Aya : 18
فَقُلۡ هَل لَّكَ إِلَىٰٓ أَن تَزَكَّىٰ
"Sai ka ce masa, Kõ zã ka so ka tsarkaka.
Aya : 19
وَأَهۡدِيَكَ إِلَىٰ رَبِّكَ فَتَخۡشَىٰ
"Kuma in shiryar da kai zuwa ga Ubangijinka domin ka ji tsoron Sa?"
Aya : 20
فَأَرَىٰهُ ٱلۡأٓيَةَ ٱلۡكُبۡرَىٰ
Sai ya nũna masa ãyar* nan mafi girma.
* Ãyar Mũsã da ta fi girma ita ce sandarsa mai zama maciji ko hannunsa mai haske kamar tõcila idan yã sanya cikin hammata yã fitar.
Aya : 21
فَكَذَّبَ وَعَصَىٰ
Sai ya ƙaryata, kuma ya sãɓa (umurni),
Aya : 22
ثُمَّ أَدۡبَرَ يَسۡعَىٰ
Sa'an nan ya jũya bãya, yanã tafiya da sauri.
Aya : 23
فَحَشَرَ فَنَادَىٰ
Sai ya yi gayya, sa'an nan ya yi kira.
Aya : 24
فَقَالَ أَنَا۠ رَبُّكُمُ ٱلۡأَعۡلَىٰ
Sai ya ce: "Nĩ ne Ubangijinku mafi ɗaudaka."
Aya : 25
فَأَخَذَهُ ٱللَّهُ نَكَالَ ٱلۡأٓخِرَةِ وَٱلۡأُولَىٰٓ
Sabõda haka Allah Ya kama shi, dõmin azãbar maganar ƙarshe da ta farko.
Aya : 26
إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَعِبۡرَةٗ لِّمَن يَخۡشَىٰٓ
Lalle ne, a cikin wannan haƙiƙa akwai abin kula ga wanda yake tsõron Allah.
Aya : 27
ءَأَنتُمۡ أَشَدُّ خَلۡقًا أَمِ ٱلسَّمَآءُۚ بَنَىٰهَا
Shin, kũ ne mafi wuyar halitta ko sama? Allah Ya gina ta.
Aya : 28
رَفَعَ سَمۡكَهَا فَسَوَّىٰهَا
Ya ɗaukaka rufinta, sa'an nan Ya daidaita ta.
Aya : 29
وَأَغۡطَشَ لَيۡلَهَا وَأَخۡرَجَ ضُحَىٰهَا
Kuma Ya duhuntar da darenta, kuma Ya fitar da hantsinta.
Aya : 30
وَٱلۡأَرۡضَ بَعۡدَ ذَٰلِكَ دَحَىٰهَآ
Kuma, ƙasa a bayan haka Ya mulmula ta.
Aya : 31
أَخۡرَجَ مِنۡهَا مَآءَهَا وَمَرۡعَىٰهَا
Ya fitar da ruwanta daga gare ta da makiyãyarta.
Aya : 32
وَٱلۡجِبَالَ أَرۡسَىٰهَا
Da duwatsu, Yã kafe ta.
Aya : 33
مَتَٰعٗا لَّكُمۡ وَلِأَنۡعَٰمِكُمۡ
Domin jiyarwa dãɗi a gare ku, kuma ga dabbõbinku.
Aya : 34
فَإِذَا جَآءَتِ ٱلطَّآمَّةُ ٱلۡكُبۡرَىٰ
To, idan uwar masĩfu, mafi girma, ta zo.
Aya : 35
يَوۡمَ يَتَذَكَّرُ ٱلۡإِنسَٰنُ مَا سَعَىٰ
Rãnar da mutum zai yi tunãnin abin da ya aikata.
Aya : 36
وَبُرِّزَتِ ٱلۡجَحِيمُ لِمَن يَرَىٰ
Kuma, a bayyana Jahĩm ga mai gani.
Aya : 37
فَأَمَّا مَن طَغَىٰ
To, amma wanda ya yi girman kai.
Aya : 38
وَءَاثَرَ ٱلۡحَيَوٰةَ ٱلدُّنۡيَا
Kuma, ya zãɓi rãyuwa ta kusa, (wato dũniya).
Aya : 39
فَإِنَّ ٱلۡجَحِيمَ هِيَ ٱلۡمَأۡوَىٰ
To, lalle ne Jahĩm, ita ce makõma.
Aya : 40
وَأَمَّا مَنۡ خَافَ مَقَامَ رَبِّهِۦ وَنَهَى ٱلنَّفۡسَ عَنِ ٱلۡهَوَىٰ
Kuma, amma wanda ya ji tsõron tsayi a gaba ga Ubangijinsa, kuma ya kange kansa daga son rai.
Aya : 41
فَإِنَّ ٱلۡجَنَّةَ هِيَ ٱلۡمَأۡوَىٰ
To, lalle ne Aljanna ita ce makõma.
Aya : 42
يَسۡـَٔلُونَكَ عَنِ ٱلسَّاعَةِ أَيَّانَ مُرۡسَىٰهَا
Sunã tambayar ka game da sa'a, wai yaushe ne matabbatarta?
Aya : 43
فِيمَ أَنتَ مِن ذِكۡرَىٰهَآ
Me ya haɗã ka da ambatonta?
Aya : 44
إِلَىٰ رَبِّكَ مُنتَهَىٰهَآ
Zuwa ga Ubangijinka ƙarshen al'amarinta yake.
Aya : 45
إِنَّمَآ أَنتَ مُنذِرُ مَن يَخۡشَىٰهَا
Kai mai gargaɗi kawai ne ga mai tsõron ta.
Aya : 46
كَأَنَّهُمۡ يَوۡمَ يَرَوۡنَهَا لَمۡ يَلۡبَثُوٓاْ إِلَّا عَشِيَّةً أَوۡ ضُحَىٰهَا
Kamar sũ a rãnar da zã su gan ta, ba su zauna ba fãce a lõkacin marẽce ko hantsinsa.
An aika shi cikin Nasara