Aya :
16
إِذۡ نَادَىٰهُ رَبُّهُۥ بِٱلۡوَادِ ٱلۡمُقَدَّسِ طُوًى
A lõkacin da Ubangijinsa Ya kirãye shi, a cikin kwari mai tsarki, wato Duwã?
Aya :
17
ٱذۡهَبۡ إِلَىٰ فِرۡعَوۡنَ إِنَّهُۥ طَغَىٰ
Ka tafi zuwa ga Fir'auna, lalle ne shi, ya ƙẽtare haddi.
Aya :
18
فَقُلۡ هَل لَّكَ إِلَىٰٓ أَن تَزَكَّىٰ
"Sai ka ce masa, Kõ zã ka so ka tsarkaka.
Aya :
19
وَأَهۡدِيَكَ إِلَىٰ رَبِّكَ فَتَخۡشَىٰ
"Kuma in shiryar da kai zuwa ga Ubangijinka domin ka ji tsoron Sa?"
Aya :
20
فَأَرَىٰهُ ٱلۡأٓيَةَ ٱلۡكُبۡرَىٰ
Sai ya nũna masa ãyar* nan mafi girma.
Aya :
21
فَكَذَّبَ وَعَصَىٰ
Sai ya ƙaryata, kuma ya sãɓa (umurni),
Aya :
22
ثُمَّ أَدۡبَرَ يَسۡعَىٰ
Sa'an nan ya jũya bãya, yanã tafiya da sauri.
Aya :
23
فَحَشَرَ فَنَادَىٰ
Sai ya yi gayya, sa'an nan ya yi kira.
Aya :
24
فَقَالَ أَنَا۠ رَبُّكُمُ ٱلۡأَعۡلَىٰ
Sai ya ce: "Nĩ ne Ubangijinku mafi ɗaudaka."
Aya :
25
فَأَخَذَهُ ٱللَّهُ نَكَالَ ٱلۡأٓخِرَةِ وَٱلۡأُولَىٰٓ
Sabõda haka Allah Ya kama shi, dõmin azãbar maganar ƙarshe da ta farko.
Aya :
26
إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَعِبۡرَةٗ لِّمَن يَخۡشَىٰٓ
Lalle ne, a cikin wannan haƙiƙa akwai abin kula ga wanda yake tsõron Allah.
Aya :
27
ءَأَنتُمۡ أَشَدُّ خَلۡقًا أَمِ ٱلسَّمَآءُۚ بَنَىٰهَا
Shin, kũ ne mafi wuyar halitta ko sama? Allah Ya gina ta.
Aya :
28
رَفَعَ سَمۡكَهَا فَسَوَّىٰهَا
Ya ɗaukaka rufinta, sa'an nan Ya daidaita ta.
Aya :
29
وَأَغۡطَشَ لَيۡلَهَا وَأَخۡرَجَ ضُحَىٰهَا
Kuma Ya duhuntar da darenta, kuma Ya fitar da hantsinta.
Aya :
30
وَٱلۡأَرۡضَ بَعۡدَ ذَٰلِكَ دَحَىٰهَآ
Kuma, ƙasa a bayan haka Ya mulmula ta.
Aya :
31
أَخۡرَجَ مِنۡهَا مَآءَهَا وَمَرۡعَىٰهَا
Ya fitar da ruwanta daga gare ta da makiyãyarta.
Aya :
32
وَٱلۡجِبَالَ أَرۡسَىٰهَا
Da duwatsu, Yã kafe ta.
Aya :
33
مَتَٰعٗا لَّكُمۡ وَلِأَنۡعَٰمِكُمۡ
Domin jiyarwa dãɗi a gare ku, kuma ga dabbõbinku.
Aya :
34
فَإِذَا جَآءَتِ ٱلطَّآمَّةُ ٱلۡكُبۡرَىٰ
To, idan uwar masĩfu, mafi girma, ta zo.
Aya :
35
يَوۡمَ يَتَذَكَّرُ ٱلۡإِنسَٰنُ مَا سَعَىٰ
Rãnar da mutum zai yi tunãnin abin da ya aikata.
Aya :
36
وَبُرِّزَتِ ٱلۡجَحِيمُ لِمَن يَرَىٰ
Kuma, a bayyana Jahĩm ga mai gani.
Aya :
37
فَأَمَّا مَن طَغَىٰ
To, amma wanda ya yi girman kai.
Aya :
38
وَءَاثَرَ ٱلۡحَيَوٰةَ ٱلدُّنۡيَا
Kuma, ya zãɓi rãyuwa ta kusa, (wato dũniya).
Aya :
39
فَإِنَّ ٱلۡجَحِيمَ هِيَ ٱلۡمَأۡوَىٰ
To, lalle ne Jahĩm, ita ce makõma.
Aya :
40
وَأَمَّا مَنۡ خَافَ مَقَامَ رَبِّهِۦ وَنَهَى ٱلنَّفۡسَ عَنِ ٱلۡهَوَىٰ
Kuma, amma wanda ya ji tsõron tsayi a gaba ga Ubangijinsa, kuma ya kange kansa daga son rai.
Aya :
41
فَإِنَّ ٱلۡجَنَّةَ هِيَ ٱلۡمَأۡوَىٰ
To, lalle ne Aljanna ita ce makõma.
Aya :
42
يَسۡـَٔلُونَكَ عَنِ ٱلسَّاعَةِ أَيَّانَ مُرۡسَىٰهَا
Sunã tambayar ka game da sa'a, wai yaushe ne matabbatarta?
Aya :
43
فِيمَ أَنتَ مِن ذِكۡرَىٰهَآ
Me ya haɗã ka da ambatonta?
Aya :
44
إِلَىٰ رَبِّكَ مُنتَهَىٰهَآ
Zuwa ga Ubangijinka ƙarshen al'amarinta yake.
Aya :
45
إِنَّمَآ أَنتَ مُنذِرُ مَن يَخۡشَىٰهَا
Kai mai gargaɗi kawai ne ga mai tsõron ta.
Aya :
46
كَأَنَّهُمۡ يَوۡمَ يَرَوۡنَهَا لَمۡ يَلۡبَثُوٓاْ إِلَّا عَشِيَّةً أَوۡ ضُحَىٰهَا
Kamar sũ a rãnar da zã su gan ta, ba su zauna ba fãce a lõkacin marẽce ko hantsinsa.