Aya :
1
عَبَسَ وَتَوَلَّىٰٓ
Yã game huska* kuma ya jũya bãya.
Aya :
2
أَن جَآءَهُ ٱلۡأَعۡمَىٰ
Sabõda makãho yã je masa.
Aya :
3
وَمَا يُدۡرِيكَ لَعَلَّهُۥ يَزَّكَّىٰٓ
To, me ya sanar da kai cẽwa watakila shi ne zai tsarkaka.
Aya :
4
أَوۡ يَذَّكَّرُ فَتَنفَعَهُ ٱلذِّكۡرَىٰٓ
Ko ya tuna, dõmin tunãwar ta amfane shi?
Aya :
5
أَمَّا مَنِ ٱسۡتَغۡنَىٰ
Amma wanda ya wadãtu da dũkiya.
Aya :
6
فَأَنتَ لَهُۥ تَصَدَّىٰ
Sa'an nan kai kuma ka ɗora bijira zuwa gare shi!
Aya :
7
وَمَا عَلَيۡكَ أَلَّا يَزَّكَّىٰ
To, me zai cũce ka idan bai tsarkaka ba?
Aya :
8
وَأَمَّا مَن جَآءَكَ يَسۡعَىٰ
Kuma, amma wanda ya zomaka yana gaugãwa.
Aya :
9
وَهُوَ يَخۡشَىٰ
Alhãli shĩ yanã jin tsõrõn Allah.
Aya :
10
فَأَنتَ عَنۡهُ تَلَهَّىٰ
Kai kuma kã shagala ga barinsa!
Aya :
11
كَلَّآ إِنَّهَا تَذۡكِرَةٞ
A'aha! Lalle ne, wannan tunãtarwa ce.
Aya :
12
فَمَن شَآءَ ذَكَرَهُۥ
Sabõda wanda ya so ya tuna Shi (Allah).
Aya :
13
فِي صُحُفٖ مُّكَرَّمَةٖ
(Tunãtarwa ce) ta cikin littafai abãban girmamãwa,
Aya :
14
مَّرۡفُوعَةٖ مُّطَهَّرَةِۭ
Abãban ɗaukakãwa, abãban tsarkakẽwa.
Aya :
15
بِأَيۡدِي سَفَرَةٖ
A cikin hannãyen mala'iku marubũta.
Aya :
16
كِرَامِۭ بَرَرَةٖ
Mãsu daraja, mãsu ɗã'a ga Allah.
Aya :
17
قُتِلَ ٱلۡإِنسَٰنُ مَآ أَكۡفَرَهُۥ
An la'ani mutum (kafiri). Mẽ yã yi kãfircinsa!
Aya :
18
مِنۡ أَيِّ شَيۡءٍ خَلَقَهُۥ
Daga wane abu, (Allah) Ya halitta shi?
Aya :
19
مِن نُّطۡفَةٍ خَلَقَهُۥ فَقَدَّرَهُۥ
Daga ɗigon maniyyi, Ya halitta shi sa'an nan Ya ƙaddarã shi (ga halaye).
Aya :
20
ثُمَّ ٱلسَّبِيلَ يَسَّرَهُۥ
Sa'an nan, hanyarsa ta fita Ya sauƙaƙe masa.
Aya :
21
ثُمَّ أَمَاتَهُۥ فَأَقۡبَرَهُۥ
Sa'an nan, Ya matar da shi sai Ya sanya shi a cikin kabari.
Aya :
22
ثُمَّ إِذَا شَآءَ أَنشَرَهُۥ
Sa'an nan, idan Ya so lalle ne zai tãyar da shi.
Aya :
23
كَلَّا لَمَّا يَقۡضِ مَآ أَمَرَهُۥ
Haƙĩƙa bai i da aikata abin da Allah Ya umurce shi ba (lõkacin sanya shi a cikin kabari).
Aya :
24
فَلۡيَنظُرِ ٱلۡإِنسَٰنُ إِلَىٰ طَعَامِهِۦٓ
To, mutum ya dũba zuwa ga abincinsa.
Aya :
25
أَنَّا صَبَبۡنَا ٱلۡمَآءَ صَبّٗا
Lalle ne Mũ, Mun zuo ruwa, zubõwa.
Aya :
26
ثُمَّ شَقَقۡنَا ٱلۡأَرۡضَ شَقّٗا
Sa'an nan, Muka tsattsãge ƙasa tsattsagewa.
Aya :
27
فَأَنۢبَتۡنَا فِيهَا حَبّٗا
Sa'an nan, Muka tsirar da ƙwaya, a cikinta.
Aya :
28
وَعِنَبٗا وَقَضۡبٗا
Da inabi da ciyãwa.
Aya :
29
وَزَيۡتُونٗا وَنَخۡلٗا
Da zaitũni da itãcen dabĩno.
Aya :
30
وَحَدَآئِقَ غُلۡبٗا
Da lambuna, mãsu yawan itãce.
Aya :
31
وَفَٰكِهَةٗ وَأَبّٗا
Da 'yã'yan itãcen marmari, da makiyãyã ta dabbõbi.
Aya :
32
مَّتَٰعٗا لَّكُمۡ وَلِأَنۡعَٰمِكُمۡ
Domin jin dãɗi a gare ku, ku da dabbobinku.
Aya :
33
فَإِذَا جَآءَتِ ٱلصَّآخَّةُ
To, idan mai tsãwa (busa ta biyu) ta zo.
Aya :
34
يَوۡمَ يَفِرُّ ٱلۡمَرۡءُ مِنۡ أَخِيهِ
Rãnar da mutum yake gudu daga ɗan'uwansa.
Aya :
35
وَأُمِّهِۦ وَأَبِيهِ
Da uwarsa da ubansa.
Aya :
36
وَصَٰحِبَتِهِۦ وَبَنِيهِ
Da mãtarsa da ɗiyansa.
Aya :
37
لِكُلِّ ٱمۡرِيٕٖ مِّنۡهُمۡ يَوۡمَئِذٖ شَأۡنٞ يُغۡنِيهِ
Ga kõwane mutum daga cikinsu, a rãnar nan akwai wani sha'ani da ya ishe shi.
Aya :
38
وُجُوهٞ يَوۡمَئِذٖ مُّسۡفِرَةٞ
Wasu huskõki, a rãnar nan, mãsu haske ne.
Aya :
39
ضَاحِكَةٞ مُّسۡتَبۡشِرَةٞ
Mãsu dãriya ne, mãsu bushãra.
Aya :
40
وَوُجُوهٞ يَوۡمَئِذٍ عَلَيۡهَا غَبَرَةٞ
Wasu huskõki, a rãnar nan, akwai ƙũra a kansu.
Aya :
41
تَرۡهَقُهَا قَتَرَةٌ
Baƙi zai rufe su.
Aya :
42
أُوْلَٰٓئِكَ هُمُ ٱلۡكَفَرَةُ ٱلۡفَجَرَةُ
Waɗannan sũ ne kãfirai fãjirai (ga ayyukansu).