Aya :
1
أَلَمۡ نَشۡرَحۡ لَكَ صَدۡرَكَ
Ba Mu bũɗa maka zũciyarka ba (dõmin ɗaukar haƙuri da fahimta)?
Aya :
2
وَوَضَعۡنَا عَنكَ وِزۡرَكَ
Kuma Muka saryar maka da nauyinka, Ashe.
Aya :
3
ٱلَّذِيٓ أَنقَضَ ظَهۡرَكَ
Wanda ya nauyayi bãyanka?
Aya :
4
وَرَفَعۡنَا لَكَ ذِكۡرَكَ
Kuma Muka ɗaukaka maka ambatonka?
Aya :
5
فَإِنَّ مَعَ ٱلۡعُسۡرِ يُسۡرًا
To, lalle ne tãre da tsananin nan akwai wani sauƙi.
Aya :
6
إِنَّ مَعَ ٱلۡعُسۡرِ يُسۡرٗا
Lalle ne tãre da tsananin nan akwai wani sauƙi.
Aya :
7
فَإِذَا فَرَغۡتَ فَٱنصَبۡ
Sabõda haka idan ka ƙãre (ibãda) sai ka kafu (kana rõƙon Allah).
Aya :
8
وَإِلَىٰ رَبِّكَ فَٱرۡغَب
Kuma zuwa ga Ubangijinka ka yi kwaɗayi.