Terjemahan Berbahasa Hausa - Abu Bakar Jomy
Terjemahan Makna Al-Qur'an al-Karim
Diterjemahkan oleh Abu Bakar Mahmud Jumi. Dikembangkan di bawah pengawasan Pusat Terjemah Ruwwād. Teks terjemahan asli masih bisa ditampilkan untuk diberi masukan, evaluasi, dan pengembangan berkelanjutan.
أَلَمۡ نَشۡرَحۡ لَكَ صَدۡرَكَ
Ba Mu bũɗa maka zũciyarka ba (dõmin ɗaukar haƙuri da fahimta)?
وَوَضَعۡنَا عَنكَ وِزۡرَكَ
Kuma Muka saryar maka da nauyinka, Ashe.
ٱلَّذِيٓ أَنقَضَ ظَهۡرَكَ
Wanda ya nauyayi bãyanka?
وَرَفَعۡنَا لَكَ ذِكۡرَكَ
Kuma Muka ɗaukaka maka ambatonka?
فَإِنَّ مَعَ ٱلۡعُسۡرِ يُسۡرًا
To, lalle ne tãre da tsananin nan akwai wani sauƙi.
إِنَّ مَعَ ٱلۡعُسۡرِ يُسۡرٗا
Lalle ne tãre da tsananin nan akwai wani sauƙi.
فَإِذَا فَرَغۡتَ فَٱنصَبۡ
Sabõda haka idan ka ƙãre (ibãda) sai ka kafu (kana rõƙon Allah).
وَإِلَىٰ رَبِّكَ فَٱرۡغَب
Kuma zuwa ga Ubangijinka ka yi kwaɗayi.
share_via