Salin sa Wikang Hausa ni Abubakr Gumi

Pagsasalin ng mga Kahulugan ng Marangal na Qur'an

Isinalin ito ni Abū Bakr Maḥmūd Jūmī. Ipinapaunlad ito sa ilalim ng pangangasiwa ng Sentro ng Pagsasalin ng Rowᾱd, at maaaring suriin ang orihinal na salin para sa layunin ng pagbibigay ng opinyon, pagsusuri, at patuloy na palilinang.

QR Code https://quran.islamcontent.com/tl/hausa_gummi

قُلۡ أَعُوذُ بِرَبِّ ٱلنَّاسِ

"Ka ce "Ina nẽman tsari ga Ubangijin mutãne."

"Ka ce "Ina nẽman tsari ga Ubangijin mutãne."

مَلِكِ ٱلنَّاسِ

"Mamallakin mutane."

"Mamallakin mutane."

إِلَٰهِ ٱلنَّاسِ

"Abin bautãwar mutãne."

"Abin bautãwar mutãne."

مِن شَرِّ ٱلۡوَسۡوَاسِ ٱلۡخَنَّاسِ

"Daga sharrin mai sanya wasuwãsi, mai ɓoyewa."[1]

[1] Shaiɗan yakan ɓõye idan ya ji an ambaci sunan Allah, dõmin haka aka yi masa suna mai ɓõyewa, wãto bã ya zuwa wurin da ake karatu da wa'azi, kamar yadda bã ya zama cikin zũciyar mutum mai ibãda da gaskiya. Ibãda ta gaskiya ita ce wadda aka yi ta kamar yadda Allah Ya ce a yi ta. Banda ibãdar bidi'a, ba ta korar Shaiɗan. Kuma da sharaɗin a yi ibãdar da kyakkyawar niyya, dõmin aikin da bãbu niyya mai kyãwu game da shi ɓãtacce ne.
"Daga sharrin mai sanya wasuwãsi, mai ɓoyewa."[1]

ٱلَّذِي يُوَسۡوِسُ فِي صُدُورِ ٱلنَّاسِ

"Wanda ke sanya wasuwãsi a cikin ƙirãzan mutane."

"Wanda ke sanya wasuwãsi a cikin ƙirãzan mutane."

مِنَ ٱلۡجِنَّةِ وَٱلنَّاسِ

"Daga aljannu da mutane."

"Daga aljannu da mutane."