Salin sa Wikang Hausa ni Abubakr Gumi
Pagsasalin ng mga Kahulugan ng Marangal na Qur'an
Isinalin ito ni Abū Bakr Maḥmūd Jūmī. Ipinapaunlad ito sa ilalim ng pangangasiwa ng Sentro ng Pagsasalin ng Rowᾱd, at maaaring suriin ang orihinal na salin para sa layunin ng pagbibigay ng opinyon, pagsusuri, at patuloy na palilinang.
أَلَمۡ نَشۡرَحۡ لَكَ صَدۡرَكَ
Ba Mu bũɗa maka zũciyarka ba (dõmin ɗaukar haƙuri da fahimta)?
وَوَضَعۡنَا عَنكَ وِزۡرَكَ
Kuma Muka saryar maka da nauyinka, Ashe.
ٱلَّذِيٓ أَنقَضَ ظَهۡرَكَ
Wanda ya nauyayi bãyanka?
وَرَفَعۡنَا لَكَ ذِكۡرَكَ
Kuma Muka ɗaukaka maka ambatonka?
فَإِنَّ مَعَ ٱلۡعُسۡرِ يُسۡرًا
To, lalle ne tãre da tsananin nan akwai wani sauƙi.
إِنَّ مَعَ ٱلۡعُسۡرِ يُسۡرٗا
Lalle ne tãre da tsananin nan akwai wani sauƙi.
فَإِذَا فَرَغۡتَ فَٱنصَبۡ
Sabõda haka idan ka ƙãre (ibãda) sai ka kafu (kana rõƙon Allah).
وَإِلَىٰ رَبِّكَ فَٱرۡغَب
Kuma zuwa ga Ubangijinka ka yi kwaɗayi.
share_via