Aya :
154
مَا لَكُمۡ كَيۡفَ تَحۡكُمُونَ
Mẽ ya same ku? Yãya kuke hukuntãwa (wannan hukunci)?
Aya :
155
أَفَلَا تَذَكَّرُونَ
Shin, bã ku tunãni?
Aya :
156
أَمۡ لَكُمۡ سُلۡطَٰنٞ مُّبِينٞ
Ko kuma kunã da wani dalĩli bayyananne ne?
Aya :
157
فَأۡتُواْ بِكِتَٰبِكُمۡ إِن كُنتُمۡ صَٰدِقِينَ
To, ku zo da littãfinku idan kun kasance mãsu gaskiya.
Aya :
158
وَجَعَلُواْ بَيۡنَهُۥ وَبَيۡنَ ٱلۡجِنَّةِ نَسَبٗاۚ وَلَقَدۡ عَلِمَتِ ٱلۡجِنَّةُ إِنَّهُمۡ لَمُحۡضَرُونَ
Kuma suka sanya nasaba a tsakãnin Sa da tsakãnin aljannu. Alhãli kuwa Lalle aljannu sun sani, "Lalle sũ, haƙĩƙa waɗanda ake halartarwa ne (a cikin wutã.)"
Aya :
159
سُبۡحَٰنَ ٱللَّهِ عَمَّا يَصِفُونَ
Tsarki ya tabbata ga Allah daga abin da suke siffantãwa.
Aya :
160
إِلَّا عِبَادَ ٱللَّهِ ٱلۡمُخۡلَصِينَ
Sai bãyin Allah waɗanda aka tsarkake.
Aya :
161
فَإِنَّكُمۡ وَمَا تَعۡبُدُونَ
To, lalle, ku da abin da kuke bautãwa,
Aya :
162
مَآ أَنتُمۡ عَلَيۡهِ بِفَٰتِنِينَ
Ba ku zama mãsu buwãya ba a gare Shi.
Aya :
163
إِلَّا مَنۡ هُوَ صَالِ ٱلۡجَحِيمِ
Sai wanda yake mai shiga babbar wutã Jahĩm.
Aya :
164
وَمَا مِنَّآ إِلَّا لَهُۥ مَقَامٞ مَّعۡلُومٞ
"Kuma bãbu kõwa daga cikinmu,* fãce yanã da matsayi sananne."
Aya :
165
وَإِنَّا لَنَحۡنُ ٱلصَّآفُّونَ
"Kuma lalle mu, haƙĩƙa, mũ ne mãsu yin sahu-sahu (dõmin ibãda)."
Aya :
166
وَإِنَّا لَنَحۡنُ ٱلۡمُسَبِّحُونَ
"Kuma lalle mũ haƙĩƙa, mũ ne mãsu yin tasbĩhi."
Aya :
167
وَإِن كَانُواْ لَيَقُولُونَ
Kuma lalle sũ, sun kasance sunã cẽwa,
Aya :
168
لَوۡ أَنَّ عِندَنَا ذِكۡرٗا مِّنَ ٱلۡأَوَّلِينَ
"Dã lalle munã da wani littãfi irin na mutãnen farko."
Aya :
169
لَكُنَّا عِبَادَ ٱللَّهِ ٱلۡمُخۡلَصِينَ
"Lalle dã mun kasance bãyin Allah waɗanda aka tsarkake."
Aya :
170
فَكَفَرُواْ بِهِۦۖ فَسَوۡفَ يَعۡلَمُونَ
Sai suka kãfirta da shi. Sabõda haka zã su sani.
Aya :
171
وَلَقَدۡ سَبَقَتۡ كَلِمَتُنَا لِعِبَادِنَا ٱلۡمُرۡسَلِينَ
Kuma lalle, haƙĩƙa kalmar Mu ta gabãta ga bãyinMu, Manzanni.
Aya :
172
إِنَّهُمۡ لَهُمُ ٱلۡمَنصُورُونَ
Lalle sũ, haƙĩƙa, sũ ne waɗanda ake taimako.
Aya :
173
وَإِنَّ جُندَنَا لَهُمُ ٱلۡغَٰلِبُونَ
Kuma lalle rundunarMu, haƙĩƙa, sũ ne marinjaya.
Aya :
174
فَتَوَلَّ عَنۡهُمۡ حَتَّىٰ حِينٖ
Sabõda haka juya daga barinsu, har a wani lõkaci.
Aya :
175
وَأَبۡصِرۡهُمۡ فَسَوۡفَ يُبۡصِرُونَ
Ka nũna musu (gaskiya), da haka zã su dinga gani.*
Aya :
176
أَفَبِعَذَابِنَا يَسۡتَعۡجِلُونَ
Shin fa, da azabarMu suke nẽman gaggãwa?
Aya :
177
فَإِذَا نَزَلَ بِسَاحَتِهِمۡ فَسَآءَ صَبَاحُ ٱلۡمُنذَرِينَ
To, idan ta sauka ga farfãjiyarsu, to, sãfiyar wadanda ake yi wa gargaɗi ta mũnana.
Aya :
178
وَتَوَلَّ عَنۡهُمۡ حَتَّىٰ حِينٖ
Kuma ka jũya daga barinsu har a wani lõkaci.
Aya :
179
وَأَبۡصِرۡ فَسَوۡفَ يُبۡصِرُونَ
Ka nũna (musu gaskiya), da haka zã su dinga nũnãwa.
Aya :
180
سُبۡحَٰنَ رَبِّكَ رَبِّ ٱلۡعِزَّةِ عَمَّا يَصِفُونَ
Tsarki ya tabbata ga Ubangijinka, Ubangijin rinjãye, daga barin abin da suke siffantãwa.
Aya :
181
وَسَلَٰمٌ عَلَى ٱلۡمُرۡسَلِينَ
Kuma aminci ya tabbata ga Manzanni.
Aya :
182
وَٱلۡحَمۡدُ لِلَّهِ رَبِّ ٱلۡعَٰلَمِينَ
Kuma gõdiya ta tabbata ga Allah Ubangijin halittu.