Aya :
1
إِذَا ٱلشَّمۡسُ كُوِّرَتۡ
Idan rãna aka shafe haskenta
Aya :
2
وَإِذَا ٱلنُّجُومُ ٱنكَدَرَتۡ
Kuma idan taurãri suka gurɓãce (wani ya shiga a cikin wani).
Aya :
3
وَإِذَا ٱلۡجِبَالُ سُيِّرَتۡ
Kuma idan duwãtsu aka tafiyar da su.
Aya :
4
وَإِذَا ٱلۡعِشَارُ عُطِّلَتۡ
Kuma idan rãƙuma mãsu cikunna* aka sakẽ su wãwai, bã ga kõwa ba.
Aya :
5
وَإِذَا ٱلۡوُحُوشُ حُشِرَتۡ
Kuma idan dabbõbin dãji aka tattara su.
Aya :
6
وَإِذَا ٱلۡبِحَارُ سُجِّرَتۡ
Kuma idan tẽkuna aka mayar da su wuta.
Aya :
7
وَإِذَا ٱلنُّفُوسُ زُوِّجَتۡ
Kuma idan rãyuka aka haɗa* su da jikunkunansu.
Aya :
8
وَإِذَا ٱلۡمَوۡءُۥدَةُ سُئِلَتۡ
Kuma idan wadda aka turbuɗe* ta da rai aka tambaye ta.
Aya :
9
بِأَيِّ ذَنۢبٖ قُتِلَتۡ
"Sabõda wane laifi ne aka kashe ta?"
Aya :
10
وَإِذَا ٱلصُّحُفُ نُشِرَتۡ
Idan takardun ayyuka aka wãtsa su (ga mãsu su).
Aya :
11
وَإِذَا ٱلسَّمَآءُ كُشِطَتۡ
Kuma idan sama aka fẽɗe ta.
Aya :
12
وَإِذَا ٱلۡجَحِيمُ سُعِّرَتۡ
Kuma idan Jahĩm aka hũra ta
Aya :
13
وَإِذَا ٱلۡجَنَّةُ أُزۡلِفَتۡ
Kuma idan Aljanna aka kusantar da ita.
Aya :
14
عَلِمَتۡ نَفۡسٞ مَّآ أَحۡضَرَتۡ
Rai ya san abin da ya halartar (a rãnar nan).
Aya :
15
فَلَآ أُقۡسِمُ بِٱلۡخُنَّسِ
To, ba sai Na yi rantsuwa da taurãri matafã* ba.
Aya :
16
ٱلۡجَوَارِ ٱلۡكُنَّسِ
Mãsu gudu suna ɓũya.
Aya :
17
وَٱلَّيۡلِ إِذَا عَسۡعَسَ
Da dare idan ya bãyar da bãya.
Aya :
18
وَٱلصُّبۡحِ إِذَا تَنَفَّسَ
Da sãfiya idan ta yi lumfashi.
Aya :
19
إِنَّهُۥ لَقَوۡلُ رَسُولٖ كَرِيمٖ
Lalle ne shi (Alƙur'ãni) haƙƙan, maganar wani manzon (Allah) ne mai girma ga Allah.
Aya :
20
ذِي قُوَّةٍ عِندَ ذِي ٱلۡعَرۡشِ مَكِينٖ
Mai ƙarfi, mai daraja a wurin Mai Al'arshi.
Aya :
21
مُّطَاعٖ ثَمَّ أَمِينٖ
Wanda ake yi wa ɗã'a (wato shugaban malã'iku) ne a can, amintacce.
Aya :
22
وَمَا صَاحِبُكُم بِمَجۡنُونٖ
Kuma abokinku ba mahaukaci ba ne.
Aya :
23
وَلَقَدۡ رَءَاهُ بِٱلۡأُفُقِ ٱلۡمُبِينِ
Kuma lalle ne, yã gan shi* a cikin sararin sama mabayyani.
Aya :
24
وَمَا هُوَ عَلَى ٱلۡغَيۡبِ بِضَنِينٖ
Kuma shi, ga gaibi* bã mai rowa ba ne.
Aya :
25
وَمَا هُوَ بِقَوۡلِ شَيۡطَٰنٖ رَّجِيمٖ
Kuma shi (Alƙur'ani) bã maganar shaiɗani, wanda aka la'ana, ba ce.
Aya :
26
فَأَيۡنَ تَذۡهَبُونَ
Shin, a inã zã ku tafi?
Aya :
27
إِنۡ هُوَ إِلَّا ذِكۡرٞ لِّلۡعَٰلَمِينَ
Lalle ne shi (Alƙur'ãni), bã kõme ba ne fãce gargaɗi ga talikai.
Aya :
28
لِمَن شَآءَ مِنكُمۡ أَن يَسۡتَقِيمَ
Ga wanda ya so, daga cikinku, ya shiryu.
Aya :
29
وَمَا تَشَآءُونَ إِلَّآ أَن يَشَآءَ ٱللَّهُ رَبُّ ٱلۡعَٰلَمِينَ
Kuma bã zã ku so ba sai idan Allah Ubangijin halitta Yã yarda.