Fassarar Ma'anonin Alqura'ni

Hausa language - Abu Bakr Jomy

Scan the qr code to link to this page

سورة التين

Lambar shafi

Aya

Bude Nassin Ayar
Bude Rataye
Share this page

Aya : 1
وَٱلتِّينِ وَٱلزَّيۡتُونِ
Inã rantsuwa da Attinu da Azzaitũn.*
* Ibn Abbas ya ce: 'Attinu shi ne masallacin Nuhu a kan Judiyyi, Azzaitun Masallacin Baitil Muƙaddas.'.
Aya : 2
وَطُورِ سِينِينَ
Da Dũr Sĩnĩna.*
* Dutsen da Allah Ya yi magana da Musa a kansa. Ma'anarsa dutse mai albarka sabõda itacen da ke kansa.
Aya : 3
وَهَٰذَا ٱلۡبَلَدِ ٱلۡأَمِينِ
Da wannan gari* amintacce.
* Gari amintacce shi ne Makkah.
Aya : 4
لَقَدۡ خَلَقۡنَا ٱلۡإِنسَٰنَ فِيٓ أَحۡسَنِ تَقۡوِيمٖ
Lalle ne, Mun halitta mutum a cikin mafi kyawon tsayuwa.
Aya : 5
ثُمَّ رَدَدۡنَٰهُ أَسۡفَلَ سَٰفِلِينَ
Sa'an nan, Muka mayar da shi mafi ƙasƙantar masu rauni
Aya : 6
إِلَّا ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ وَعَمِلُواْ ٱلصَّٰلِحَٰتِ فَلَهُمۡ أَجۡرٌ غَيۡرُ مَمۡنُونٖ
Face waɗanda suka yi imani, kuma suka aikata ayyukan ƙwarai, saboda haka suna da sakamako wanda bã ya yankewa.
Aya : 7
فَمَا يُكَذِّبُكَ بَعۡدُ بِٱلدِّينِ
To, bãyan haka mẽ ya sanya ka ka ƙaryata sakamako (wanda za a yi a bãyan Tãshin ¡iyãma)?
Aya : 8
أَلَيۡسَ ٱللَّهُ بِأَحۡكَمِ ٱلۡحَٰكِمِينَ
Ashe Allah bã Shi ne Mafi mãsu hukunci kyãwon hukunci ba?*
* Ana son wanda ya karanta sũrar har ƙarshe ya ce بلى ,wato na'am, Allah Ya fi kowa kyãwon hukunci.
An aika shi cikin Nasara