Aya :
1
وَٱلتِّينِ وَٱلزَّيۡتُونِ
Inã rantsuwa da Attinu da Azzaitũn.*
Aya :
2
وَطُورِ سِينِينَ
Da Dũr Sĩnĩna.*
Aya :
3
وَهَٰذَا ٱلۡبَلَدِ ٱلۡأَمِينِ
Da wannan gari* amintacce.
Aya :
4
لَقَدۡ خَلَقۡنَا ٱلۡإِنسَٰنَ فِيٓ أَحۡسَنِ تَقۡوِيمٖ
Lalle ne, Mun halitta mutum a cikin mafi kyawon tsayuwa.
Aya :
5
ثُمَّ رَدَدۡنَٰهُ أَسۡفَلَ سَٰفِلِينَ
Sa'an nan, Muka mayar da shi mafi ƙasƙantar masu rauni
Aya :
6
إِلَّا ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ وَعَمِلُواْ ٱلصَّٰلِحَٰتِ فَلَهُمۡ أَجۡرٌ غَيۡرُ مَمۡنُونٖ
Face waɗanda suka yi imani, kuma suka aikata ayyukan ƙwarai, saboda haka suna da sakamako wanda bã ya yankewa.
Aya :
7
فَمَا يُكَذِّبُكَ بَعۡدُ بِٱلدِّينِ
To, bãyan haka mẽ ya sanya ka ka ƙaryata sakamako (wanda za a yi a bãyan Tãshin ¡iyãma)?
Aya :
8
أَلَيۡسَ ٱللَّهُ بِأَحۡكَمِ ٱلۡحَٰكِمِينَ
Ashe Allah bã Shi ne Mafi mãsu hukunci kyãwon hukunci ba?*