Aya :
1
سَبِّحِ ٱسۡمَ رَبِّكَ ٱلۡأَعۡلَى
Ka tsarkake sũnan Ubangijinka Mafi ɗaukaka.
Aya :
2
ٱلَّذِي خَلَقَ فَسَوَّىٰ
Wanda Yã yi halitta sa'an nan Ya daidaita abin halittar.
Aya :
3
وَٱلَّذِي قَدَّرَ فَهَدَىٰ
Kuma Wanda Ya ƙaddara (abin da Ya so) sannan Ya shiryar, (da mutum ga hanyar alhẽri da ta sharri).
Aya :
4
وَٱلَّذِيٓ أَخۡرَجَ ٱلۡمَرۡعَىٰ
Kuma Wanda Ya fitar da makiyãyã.
Aya :
5
فَجَعَلَهُۥ غُثَآءً أَحۡوَىٰ
Sa'an nan Ya mayar da ita ƙeƙasassa, baƙa.
Aya :
6
سَنُقۡرِئُكَ فَلَا تَنسَىٰٓ
Za mu karantar da kai (Alƙur'ãni) sabõda haka bã zã ka mantã (shi) ba.
Aya :
7
إِلَّا مَا شَآءَ ٱللَّهُۚ إِنَّهُۥ يَعۡلَمُ ٱلۡجَهۡرَ وَمَا يَخۡفَىٰ
Fãce abin da Allah Ya so, lalle ne Shi (Allah) Ya san bayyane da abin da yake bõye.
Aya :
8
وَنُيَسِّرُكَ لِلۡيُسۡرَىٰ
Kuma za Mu sauƙaƙe maka (al'amari) zuwa ga (Shari'a) mai sauƙi.
Aya :
9
فَذَكِّرۡ إِن نَّفَعَتِ ٱلذِّكۡرَىٰ
Sabõda baka, ka tunãtar, idan tunatarwa zã ta yi amfãni.
Aya :
10
سَيَذَّكَّرُ مَن يَخۡشَىٰ
Wanda yake tsõron (Allah) Zai tuna.
Aya :
11
وَيَتَجَنَّبُهَا ٱلۡأَشۡقَى
Kuma shaƙiyyi, zai nisanceta,
Aya :
12
ٱلَّذِي يَصۡلَى ٱلنَّارَ ٱلۡكُبۡرَىٰ
Wanda zai shiga wutar da tã fi girma.
Aya :
13
ثُمَّ لَا يَمُوتُ فِيهَا وَلَا يَحۡيَىٰ
Sa'an nan bã zai mutu ba a cikinta, kuma bã zai rãyu ba.
Aya :
14
قَدۡ أَفۡلَحَ مَن تَزَكَّىٰ
Lalle ne wanda ya tsarkaka (da ĩmãni) yã sãmu babban rabo.
Aya :
15
وَذَكَرَ ٱسۡمَ رَبِّهِۦ فَصَلَّىٰ
Kuma ya ambaci sũnan* Ubangijinsa, sa'an nan yã yi salla.