Fassarar Ma'anonin Alqura'ni

Hausa language - Abu Bakr Jomy

Scan the qr code to link to this page

سورة الحاقة

Lambar shafi

Aya

Bude Nassin Ayar
Bude Rataye
Share this page

Aya : 1
ٱلۡحَآقَّةُ
Kiran gaskiya!
Aya : 2
مَا ٱلۡحَآقَّةُ
Mẽne ne kiran gaskiya?
Aya : 3
وَمَآ أَدۡرَىٰكَ مَا ٱلۡحَآقَّةُ
Kuma mẽ ya sanar da kai abin da ake cẽwa kiran gaskiya?
Aya : 4
كَذَّبَتۡ ثَمُودُ وَعَادُۢ بِٱلۡقَارِعَةِ
Samũdãwa da Ãdãwa sun ƙaryatar da kiran gaskiya mai dũkar zũciya!
Aya : 5
فَأَمَّا ثَمُودُ فَأُهۡلِكُواْ بِٱلطَّاغِيَةِ
To, amma Samũdãwa to, an halakãsu da tsãwa mai tsanani.
Aya : 6
وَأَمَّا عَادٞ فَأُهۡلِكُواْ بِرِيحٖ صَرۡصَرٍ عَاتِيَةٖ
Kuma amma Ãdãwa to, an halaka su da wata iska mai tsananin sauti wadda ta ƙẽtare haddi.
Aya : 7
سَخَّرَهَا عَلَيۡهِمۡ سَبۡعَ لَيَالٖ وَثَمَٰنِيَةَ أَيَّامٍ حُسُومٗاۖ فَتَرَى ٱلۡقَوۡمَ فِيهَا صَرۡعَىٰ كَأَنَّهُمۡ أَعۡجَازُ نَخۡلٍ خَاوِيَةٖ
(Allah) Ya hõre ta a kansu a cikin dare bakwai da yini takwas, biye da jũna, sabõda haka, kana ganin mutãne a cikinta kwance. Kamar sũ ƙirãruwan dabĩno ne, waɗanda suka fãɗi.
Aya : 8
فَهَلۡ تَرَىٰ لَهُم مِّنۢ بَاقِيَةٖ
To, kõ kanã ganin abin da ya yi saurã daga cikinsu?

Aya : 9
وَجَآءَ فِرۡعَوۡنُ وَمَن قَبۡلَهُۥ وَٱلۡمُؤۡتَفِكَٰتُ بِٱلۡخَاطِئَةِ
Kuma Fir'auna yã zo da waɗanda ke gabãninsa, da waɗannan da aka kife ƙasarsu, sabõda laifi.
Aya : 10
فَعَصَوۡاْ رَسُولَ رَبِّهِمۡ فَأَخَذَهُمۡ أَخۡذَةٗ رَّابِيَةً
Dõmin sun sãɓã wa manzon Ubangijinsu, sabõda haka ya kãmã su da wani irin kãmu mai ƙãruwar (tsanani).
Aya : 11
إِنَّا لَمَّا طَغَا ٱلۡمَآءُ حَمَلۡنَٰكُمۡ فِي ٱلۡجَارِيَةِ
Lalle ne, Mũ, a lõkacin da ruwa ya ƙẽtare haddi, Munɗauke aaku a cikin jirgin ruwan nan.
Aya : 12
لِنَجۡعَلَهَا لَكُمۡ تَذۡكِرَةٗ وَتَعِيَهَآ أُذُنٞ وَٰعِيَةٞ
Dõmin Mu sanya shi, gare ku abin tunãwa kuma wani kunne mai kiyayewa ya kiyaye (shi).
Aya : 13
فَإِذَا نُفِخَ فِي ٱلصُّورِ نَفۡخَةٞ وَٰحِدَةٞ
To, idan an yi bũsa a cikin ƙaho, bũsa ɗaya.
Aya : 14
وَحُمِلَتِ ٱلۡأَرۡضُ وَٱلۡجِبَالُ فَدُكَّتَا دَكَّةٗ وَٰحِدَةٗ
Kuma aka ɗauki ƙasa da duwãtsu, kuma aka niƙa su niƙãwa ɗaya.
Aya : 15
فَيَوۡمَئِذٖ وَقَعَتِ ٱلۡوَاقِعَةُ
A ran nan, mai aukuwa zã ta auku.
Aya : 16
وَٱنشَقَّتِ ٱلسَّمَآءُ فَهِيَ يَوۡمَئِذٖ وَاهِيَةٞ
Kuma sama zã ta tsãge, dõmin ita a ran nan, mai rauni ce.
Aya : 17
وَٱلۡمَلَكُ عَلَىٰٓ أَرۡجَآئِهَاۚ وَيَحۡمِلُ عَرۡشَ رَبِّكَ فَوۡقَهُمۡ يَوۡمَئِذٖ ثَمَٰنِيَةٞ
Kuma malã'iku (su bayyana) a kan sãsanninta, kuma wasu (malã'iku) takwas na ɗauke da Al'arshin Ubangijinka, a sama da su, a wannan rãnar.
Aya : 18
يَوۡمَئِذٖ تُعۡرَضُونَ لَا تَخۡفَىٰ مِنكُمۡ خَافِيَةٞ
A rãnar nan zã a bijirã ku (dõmin hisãbi), bãbu wani rai, mai ɓoyewa, daga cikinku, wanda zai iya ɓõyẽwa.
Aya : 19
فَأَمَّا مَنۡ أُوتِيَ كِتَٰبَهُۥ بِيَمِينِهِۦ فَيَقُولُ هَآؤُمُ ٱقۡرَءُواْ كِتَٰبِيَهۡ
To, amma wanda aka bai wa littãfinsa a dãmansa, sai ya ce wa (makusantansa), "Ku karɓa, ku karanta littafina."
Aya : 20
إِنِّي ظَنَنتُ أَنِّي مُلَٰقٍ حِسَابِيَهۡ
"Lalle ne ni, nã tabbata cewa ni mai haɗuwa da hisãbina ne."
Aya : 21
فَهُوَ فِي عِيشَةٖ رَّاضِيَةٖ
Sabõda haka, shi yana cikin wata rãyuwa yardadda.
Aya : 22
فِي جَنَّةٍ عَالِيَةٖ
A cikin Aljanna maɗaukakiya.
Aya : 23
قُطُوفُهَا دَانِيَةٞ
Nunannun 'yã'yan itãcenta makusantã ne (ga mai son ɗĩba),
Aya : 24
كُلُواْ وَٱشۡرَبُواْ هَنِيٓـَٔۢا بِمَآ أَسۡلَفۡتُمۡ فِي ٱلۡأَيَّامِ ٱلۡخَالِيَةِ
(Ana ce musu) "Ku ci, kuma ku sha a cikin ni'ima, sabõda abin da kuka gabãtar a cikin kwãnukan da suka shige."
Aya : 25
وَأَمَّا مَنۡ أُوتِيَ كِتَٰبَهُۥ بِشِمَالِهِۦ فَيَقُولُ يَٰلَيۡتَنِي لَمۡ أُوتَ كِتَٰبِيَهۡ
Kuma wanda aka bai wa littãfinsa ga hagunsa, sai ya ce: "Kaitona, ba a kãwo mini littãfina ba!"
Aya : 26
وَلَمۡ أَدۡرِ مَا حِسَابِيَهۡ
"Kuma ban san abin da (ke sakamakon) hisãbina ba!"
Aya : 27
يَٰلَيۡتَهَا كَانَتِ ٱلۡقَاضِيَةَ
"In dã dai ita, tã kasance mai halakã ni gabã ɗaya ce!
Aya : 28
مَآ أَغۡنَىٰ عَنِّي مَالِيَهۡۜ
"Dukiyãta ba ta wadatar da ni ba!"
Aya : 29
هَلَكَ عَنِّي سُلۡطَٰنِيَهۡ
"Ĩkona ya ɓace mini!"
Aya : 30
خُذُوهُ فَغُلُّوهُ
(Sai a ce wa malã'iku) "Ku kãmã shi, sa'an nan ku sanyã shi a cikin ƙuƙumi."
Aya : 31
ثُمَّ ٱلۡجَحِيمَ صَلُّوهُ
"Sa'an nan, a cikin Jahĩm, ku ƙõna shi."
Aya : 32
ثُمَّ فِي سِلۡسِلَةٖ ذَرۡعُهَا سَبۡعُونَ ذِرَاعٗا فَٱسۡلُكُوهُ
"Sa'an nan, acikin sarƙa, tsawonta zirã'i saba'in, sai ku sanya shi."
Aya : 33
إِنَّهُۥ كَانَ لَا يُؤۡمِنُ بِٱللَّهِ ٱلۡعَظِيمِ
"Lalle ne, shi ya kasance ba ya yin ĩmãni da Allah, Mai girma!"
Aya : 34
وَلَا يَحُضُّ عَلَىٰ طَعَامِ ٱلۡمِسۡكِينِ
"Kuma ba ya kwaɗaitarwa ga (bãyar da) abincin matalauci!"

Aya : 35
فَلَيۡسَ لَهُ ٱلۡيَوۡمَ هَٰهُنَا حَمِيمٞ
"Sabõda haka, a yau, a nan, bã ya da masõyi."
Aya : 36
وَلَا طَعَامٌ إِلَّا مِنۡ غِسۡلِينٖ
"Kuma bãbu wani abinci, sai daga (itãcen) gislĩn."
Aya : 37
لَّا يَأۡكُلُهُۥٓ إِلَّا ٱلۡخَٰطِـُٔونَ
"Bãbu mai cin sa sai mãsu ganganci."
Aya : 38
فَلَآ أُقۡسِمُ بِمَا تُبۡصِرُونَ
To, ba sai Nã yi rantsuwa da abin da kuke iya gani ba,
Aya : 39
وَمَا لَا تُبۡصِرُونَ
Da abin da bã ku iya gani.
Aya : 40
إِنَّهُۥ لَقَوۡلُ رَسُولٖ كَرِيمٖ
Lalle ne, shi (Alƙur'ani) tabbas maganar wani manzo (Jibirilu) mai daraja ne.
Aya : 41
وَمَا هُوَ بِقَوۡلِ شَاعِرٖۚ قَلِيلٗا مَّا تُؤۡمِنُونَ
Kuma shi ba maganar wani mawãƙi ba ne. Kaɗan ƙwarai zã ku gaskata.
Aya : 42
وَلَا بِقَوۡلِ كَاهِنٖۚ قَلِيلٗا مَّا تَذَكَّرُونَ
Kuma bã maganar bõka ba ne. Kaɗan ƙwarai zã ku iya tunãwa.
Aya : 43
تَنزِيلٞ مِّن رَّبِّ ٱلۡعَٰلَمِينَ
Abin saukarwã ne daga Ubangijin halitta duka.
Aya : 44
وَلَوۡ تَقَوَّلَ عَلَيۡنَا بَعۡضَ ٱلۡأَقَاوِيلِ
Kuma dã (Muhammadu) yã faɗi wata maganã, yã jingina ta garẽ Mu.
Aya : 45
لَأَخَذۡنَا مِنۡهُ بِٱلۡيَمِينِ
Dã Mun kãma shi da dãma.
Aya : 46
ثُمَّ لَقَطَعۡنَا مِنۡهُ ٱلۡوَتِينَ
sa'an nan, lalle ne, dã Mun kãtse masa lakã.
Aya : 47
فَمَا مِنكُم مِّنۡ أَحَدٍ عَنۡهُ حَٰجِزِينَ
Kuma daga cikinku bãbu wasu mãsu iya kãre (azãbar Mu) daga gare shi.
Aya : 48
وَإِنَّهُۥ لَتَذۡكِرَةٞ لِّلۡمُتَّقِينَ
Kuma lalle ne shi (Alƙur'ãni) tanãtarwa ce ga mãsu taƙawa.
Aya : 49
وَإِنَّا لَنَعۡلَمُ أَنَّ مِنكُم مُّكَذِّبِينَ
Kuma lalle, ne Mũ, wallahi Munã sane da cẽwa daga cikinku alwwai mãsu ƙaryatãwa.
Aya : 50
وَإِنَّهُۥ لَحَسۡرَةٌ عَلَى ٱلۡكَٰفِرِينَ
Kuma lalle ne shi (Alƙarãni) wallahi baƙin ciki ne ga kãfirai.
Aya : 51
وَإِنَّهُۥ لَحَقُّ ٱلۡيَقِينِ
Kuma lalle, ne shi gaskiya ce ta yaƙini.
Aya : 52
فَسَبِّحۡ بِٱسۡمِ رَبِّكَ ٱلۡعَظِيمِ
Sabõda haka, ka tsarkake sũnan Ubangjinka, mai girma.
An aika shi cikin Nasara