Aya :
9
وَجَآءَ فِرۡعَوۡنُ وَمَن قَبۡلَهُۥ وَٱلۡمُؤۡتَفِكَٰتُ بِٱلۡخَاطِئَةِ
Kuma Fir'auna yã zo da waɗanda ke gabãninsa, da waɗannan da aka kife ƙasarsu, sabõda laifi.
Aya :
10
فَعَصَوۡاْ رَسُولَ رَبِّهِمۡ فَأَخَذَهُمۡ أَخۡذَةٗ رَّابِيَةً
Dõmin sun sãɓã wa manzon Ubangijinsu, sabõda haka ya kãmã su da wani irin kãmu mai ƙãruwar (tsanani).
Aya :
11
إِنَّا لَمَّا طَغَا ٱلۡمَآءُ حَمَلۡنَٰكُمۡ فِي ٱلۡجَارِيَةِ
Lalle ne, Mũ, a lõkacin da ruwa ya ƙẽtare haddi, Munɗauke aaku a cikin jirgin ruwan nan.
Aya :
12
لِنَجۡعَلَهَا لَكُمۡ تَذۡكِرَةٗ وَتَعِيَهَآ أُذُنٞ وَٰعِيَةٞ
Dõmin Mu sanya shi, gare ku abin tunãwa kuma wani kunne mai kiyayewa ya kiyaye (shi).
Aya :
13
فَإِذَا نُفِخَ فِي ٱلصُّورِ نَفۡخَةٞ وَٰحِدَةٞ
To, idan an yi bũsa a cikin ƙaho, bũsa ɗaya.
Aya :
14
وَحُمِلَتِ ٱلۡأَرۡضُ وَٱلۡجِبَالُ فَدُكَّتَا دَكَّةٗ وَٰحِدَةٗ
Kuma aka ɗauki ƙasa da duwãtsu, kuma aka niƙa su niƙãwa ɗaya.
Aya :
15
فَيَوۡمَئِذٖ وَقَعَتِ ٱلۡوَاقِعَةُ
A ran nan, mai aukuwa zã ta auku.
Aya :
16
وَٱنشَقَّتِ ٱلسَّمَآءُ فَهِيَ يَوۡمَئِذٖ وَاهِيَةٞ
Kuma sama zã ta tsãge, dõmin ita a ran nan, mai rauni ce.
Aya :
17
وَٱلۡمَلَكُ عَلَىٰٓ أَرۡجَآئِهَاۚ وَيَحۡمِلُ عَرۡشَ رَبِّكَ فَوۡقَهُمۡ يَوۡمَئِذٖ ثَمَٰنِيَةٞ
Kuma malã'iku (su bayyana) a kan sãsanninta, kuma wasu (malã'iku) takwas na ɗauke da Al'arshin Ubangijinka, a sama da su, a wannan rãnar.
Aya :
18
يَوۡمَئِذٖ تُعۡرَضُونَ لَا تَخۡفَىٰ مِنكُمۡ خَافِيَةٞ
A rãnar nan zã a bijirã ku (dõmin hisãbi), bãbu wani rai, mai ɓoyewa, daga cikinku, wanda zai iya ɓõyẽwa.
Aya :
19
فَأَمَّا مَنۡ أُوتِيَ كِتَٰبَهُۥ بِيَمِينِهِۦ فَيَقُولُ هَآؤُمُ ٱقۡرَءُواْ كِتَٰبِيَهۡ
To, amma wanda aka bai wa littãfinsa a dãmansa, sai ya ce wa (makusantansa), "Ku karɓa, ku karanta littafina."
Aya :
20
إِنِّي ظَنَنتُ أَنِّي مُلَٰقٍ حِسَابِيَهۡ
"Lalle ne ni, nã tabbata cewa ni mai haɗuwa da hisãbina ne."
Aya :
21
فَهُوَ فِي عِيشَةٖ رَّاضِيَةٖ
Sabõda haka, shi yana cikin wata rãyuwa yardadda.
Aya :
22
فِي جَنَّةٍ عَالِيَةٖ
A cikin Aljanna maɗaukakiya.
Aya :
23
قُطُوفُهَا دَانِيَةٞ
Nunannun 'yã'yan itãcenta makusantã ne (ga mai son ɗĩba),
Aya :
24
كُلُواْ وَٱشۡرَبُواْ هَنِيٓـَٔۢا بِمَآ أَسۡلَفۡتُمۡ فِي ٱلۡأَيَّامِ ٱلۡخَالِيَةِ
(Ana ce musu) "Ku ci, kuma ku sha a cikin ni'ima, sabõda abin da kuka gabãtar a cikin kwãnukan da suka shige."
Aya :
25
وَأَمَّا مَنۡ أُوتِيَ كِتَٰبَهُۥ بِشِمَالِهِۦ فَيَقُولُ يَٰلَيۡتَنِي لَمۡ أُوتَ كِتَٰبِيَهۡ
Kuma wanda aka bai wa littãfinsa ga hagunsa, sai ya ce: "Kaitona, ba a kãwo mini littãfina ba!"
Aya :
26
وَلَمۡ أَدۡرِ مَا حِسَابِيَهۡ
"Kuma ban san abin da (ke sakamakon) hisãbina ba!"
Aya :
27
يَٰلَيۡتَهَا كَانَتِ ٱلۡقَاضِيَةَ
"In dã dai ita, tã kasance mai halakã ni gabã ɗaya ce!
Aya :
28
مَآ أَغۡنَىٰ عَنِّي مَالِيَهۡۜ
"Dukiyãta ba ta wadatar da ni ba!"
Aya :
29
هَلَكَ عَنِّي سُلۡطَٰنِيَهۡ
"Ĩkona ya ɓace mini!"
Aya :
30
خُذُوهُ فَغُلُّوهُ
(Sai a ce wa malã'iku) "Ku kãmã shi, sa'an nan ku sanyã shi a cikin ƙuƙumi."
Aya :
31
ثُمَّ ٱلۡجَحِيمَ صَلُّوهُ
"Sa'an nan, a cikin Jahĩm, ku ƙõna shi."
Aya :
32
ثُمَّ فِي سِلۡسِلَةٖ ذَرۡعُهَا سَبۡعُونَ ذِرَاعٗا فَٱسۡلُكُوهُ
"Sa'an nan, acikin sarƙa, tsawonta zirã'i saba'in, sai ku sanya shi."
Aya :
33
إِنَّهُۥ كَانَ لَا يُؤۡمِنُ بِٱللَّهِ ٱلۡعَظِيمِ
"Lalle ne, shi ya kasance ba ya yin ĩmãni da Allah, Mai girma!"
Aya :
34
وَلَا يَحُضُّ عَلَىٰ طَعَامِ ٱلۡمِسۡكِينِ
"Kuma ba ya kwaɗaitarwa ga (bãyar da) abincin matalauci!"