Aya :
1
وَٱلضُّحَىٰ
Inã rantsuwa da hantsi.
Aya :
2
وَٱلَّيۡلِ إِذَا سَجَىٰ
Da dare a lõkacin da ya rufe (da duhunsa).
Aya :
3
مَا وَدَّعَكَ رَبُّكَ وَمَا قَلَىٰ
Ubangijinka bai yi maka bankwana ba, kuma bai ƙĩ kaba.
Aya :
4
وَلَلۡأٓخِرَةُ خَيۡرٞ لَّكَ مِنَ ٱلۡأُولَىٰ
Kuma lalle ta ƙarshe* ce mafi alheri a gare ka daga ta farko.
Aya :
5
وَلَسَوۡفَ يُعۡطِيكَ رَبُّكَ فَتَرۡضَىٰٓ
Kuma lalle ne, Ubangijinka zai yi ta bã ka kyauta sai ka yarda.
Aya :
6
أَلَمۡ يَجِدۡكَ يَتِيمٗا فَـَٔاوَىٰ
Ashe, bai sãme ka marãya ba, sa'an nan Ya yi maka makõma?
Aya :
7
وَوَجَدَكَ ضَآلّٗا فَهَدَىٰ
Kuma Ya sãme ka bã ka da shari'ã, sai Ya shiryar da kai?
Aya :
8
وَوَجَدَكَ عَآئِلٗا فَأَغۡنَىٰ
Kuma Ya sãme ka matalauci, sai Ya wadãtã ka?
Aya :
9
فَأَمَّا ٱلۡيَتِيمَ فَلَا تَقۡهَرۡ
Sabõda haka, amma marãya, to, kada ka rinjãye shi.
Aya :
10
وَأَمَّا ٱلسَّآئِلَ فَلَا تَنۡهَرۡ
Kuma amma mai tambaya, kada ka yi masa tsãwa.
Aya :
11
وَأَمَّا بِنِعۡمَةِ رَبِّكَ فَحَدِّثۡ
Kuma amma ni'imar Ubangijinka, sai ka faɗa (dõmin gõdiya).