Fassarar Ma'anonin Alqura'ni

Hausa language - Abu Bakr Jomy

Scan the qr code to link to this page

سورة الغاشية

Lambar shafi

Aya

Bude Nassin Ayar
Bude Rataye
Share this page

Aya : 1
هَلۡ أَتَىٰكَ حَدِيثُ ٱلۡغَٰشِيَةِ
Lalle ne labãrin (¡iyãma) mai rufe mutãne da tsoronta yã zo maka?
Aya : 2
وُجُوهٞ يَوۡمَئِذٍ خَٰشِعَةٌ
Wasu huskõki a rãnar nan ƙasƙantattu ne.
Aya : 3
عَامِلَةٞ نَّاصِبَةٞ
Mãsu aikin wahala ne, mãsu gajiya.
Aya : 4
تَصۡلَىٰ نَارًا حَامِيَةٗ
Zã su shiga wata wuta mai zãfi.
Aya : 5
تُسۡقَىٰ مِنۡ عَيۡنٍ ءَانِيَةٖ
Ana shãyar da su daga wani marmaro mai zãfin ruwa.
Aya : 6
لَّيۡسَ لَهُمۡ طَعَامٌ إِلَّا مِن ضَرِيعٖ
Ba su da wani abinci fãce dai daga danyi.
Aya : 7
لَّا يُسۡمِنُ وَلَا يُغۡنِي مِن جُوعٖ
Bã ya sanya ƙiba, kuma bã zai wadãtar daga yunwa ba.
Aya : 8
وُجُوهٞ يَوۡمَئِذٖ نَّاعِمَةٞ
Wasu huskõki a rãnar nan mãsu ni'ima ne.
Aya : 9
لِّسَعۡيِهَا رَاضِيَةٞ
Game da aikinsu, masu yarda ne.
Aya : 10
فِي جَنَّةٍ عَالِيَةٖ
(Suna) a cikin Aljanna maɗaukakiya.
Aya : 11
لَّا تَسۡمَعُ فِيهَا لَٰغِيَةٗ
Bã zã su ji yãsassar magana ba, a cikinta.
Aya : 12
فِيهَا عَيۡنٞ جَارِيَةٞ
A cikinta akwai marmaro mai gudãna.
Aya : 13
فِيهَا سُرُرٞ مَّرۡفُوعَةٞ
A cikinta akwai gadãje maɗaukaka.
Aya : 14
وَأَكۡوَابٞ مَّوۡضُوعَةٞ
Da kõfuna ar'aje.
Aya : 15
وَنَمَارِقُ مَصۡفُوفَةٞ
Da filõli* jẽre,
* Matãsan kai.
Aya : 16
وَزَرَابِيُّ مَبۡثُوثَةٌ
Da katifu shimfiɗe.
Aya : 17
أَفَلَا يَنظُرُونَ إِلَى ٱلۡإِبِلِ كَيۡفَ خُلِقَتۡ
Ashe to bã zã su dũbãwa ba ga rãƙumã yadda aka halitta su?
Aya : 18
وَإِلَى ٱلسَّمَآءِ كَيۡفَ رُفِعَتۡ
Da zuwa ga sama yadda aka ɗaukaka ta?
Aya : 19
وَإِلَى ٱلۡجِبَالِ كَيۡفَ نُصِبَتۡ
Da zuwa ga duwãtsu yadda aka kafa su?
Aya : 20
وَإِلَى ٱلۡأَرۡضِ كَيۡفَ سُطِحَتۡ
Da zuwa ga ƙasa yadda aka shimfiɗã ta?
Aya : 21
فَذَكِّرۡ إِنَّمَآ أَنتَ مُذَكِّرٞ
sabõda haka, ka yi wa'azi, kai mai yin wa'azi ne kawai.
Aya : 22
لَّسۡتَ عَلَيۡهِم بِمُصَيۡطِرٍ
Ba ka zama mai ĩkon tanƙwasãwa a kansu ba.
Aya : 23
إِلَّا مَن تَوَلَّىٰ وَكَفَرَ
Fãce dai duk wanda ya jũya bãya, kuma ya kãfirta.
Aya : 24
فَيُعَذِّبُهُ ٱللَّهُ ٱلۡعَذَابَ ٱلۡأَكۡبَرَ
To, Allah zai yi masa azãba, azãbar nan da take mafi girma.
Aya : 25
إِنَّ إِلَيۡنَآ إِيَابَهُمۡ
Lalle ne, zuwa gare Mu kõmõwarsu take.
Aya : 26
ثُمَّ إِنَّ عَلَيۡنَا حِسَابَهُم
Sa'an nan lalle ne aikinMu ne Mu yi musu hisãbi.
An aika shi cikin Nasara