Aya :
1
إِذَا ٱلسَّمَآءُ ٱنفَطَرَتۡ
Idan sama ta tsãge.
Aya :
2
وَإِذَا ٱلۡكَوَاكِبُ ٱنتَثَرَتۡ
Kuma idan taurãri suka wãtse.
Aya :
3
وَإِذَا ٱلۡبِحَارُ فُجِّرَتۡ
Kuma idan tẽkuna aka facce su.
Aya :
4
وَإِذَا ٱلۡقُبُورُ بُعۡثِرَتۡ
Kuma idan kaburbura aka tõne su.
Aya :
5
عَلِمَتۡ نَفۡسٞ مَّا قَدَّمَتۡ وَأَخَّرَتۡ
Rai yã san abin da ya gabatar, da abin da yã jinkirtar.
Aya :
6
يَٰٓأَيُّهَا ٱلۡإِنسَٰنُ مَا غَرَّكَ بِرَبِّكَ ٱلۡكَرِيمِ
Yã kai mutum! Mẽ ya rũɗe ka game da Ubangijinka, Mai karamci.
Aya :
7
ٱلَّذِي خَلَقَكَ فَسَوَّىٰكَ فَعَدَلَكَ
Wanda Ya halitta ka sa'an nan ya daidaitã ka, Ya kuma tsakaitã ka.
Aya :
8
فِيٓ أَيِّ صُورَةٖ مَّا شَآءَ رَكَّبَكَ
A cikin kõwace irin sũra Ya so Ya ginã ka a kanta.
Aya :
9
كَلَّا بَلۡ تُكَذِّبُونَ بِٱلدِّينِ
A'aha, bã haka ba, kuna ƙaryatãwa game da sakamako!
Aya :
10
وَإِنَّ عَلَيۡكُمۡ لَحَٰفِظِينَ
Lalle ne, a kanku, haƙiƙa akwai matsara.
Aya :
11
كِرَامٗا كَٰتِبِينَ
Mãsu daraja, marubũta.
Aya :
12
يَعۡلَمُونَ مَا تَفۡعَلُونَ
Sunã sanin abin da kuke aikatãwa.
Aya :
13
إِنَّ ٱلۡأَبۡرَارَ لَفِي نَعِيمٖ
Lalle ne, mãsu ɗã'ã ga Allah, dãhir, suna cikin ni'ima.
Aya :
14
وَإِنَّ ٱلۡفُجَّارَ لَفِي جَحِيمٖ
Kuma lalle ne, fãjirai, dãhir, sunã cikin Jahĩm.
Aya :
15
يَصۡلَوۡنَهَا يَوۡمَ ٱلدِّينِ
Zã su shigẽ ta a rãnar sakamako.
Aya :
16
وَمَا هُمۡ عَنۡهَا بِغَآئِبِينَ
Bã zã su faku daga gare ta ba.
Aya :
17
وَمَآ أَدۡرَىٰكَ مَا يَوۡمُ ٱلدِّينِ
Kuma mẽ ya sanar da kai abin da ake cẽ wa ranar sakamako?
Aya :
18
ثُمَّ مَآ أَدۡرَىٰكَ مَا يَوۡمُ ٱلدِّينِ
Sa'an nan, mẽ ya sanar da kai abin da ake cẽ wa rãnar sakamako?
Aya :
19
يَوۡمَ لَا تَمۡلِكُ نَفۡسٞ لِّنَفۡسٖ شَيۡـٔٗاۖ وَٱلۡأَمۡرُ يَوۡمَئِذٖ لِّلَّهِ
Rãnã ce da wani rai ba ya iya mallakar kõme dõmin wani rai al'amari, a rãnar nan, ga Allah (ɗai) yake.