Aya :
51
ثُمَّ إِنَّكُمۡ أَيُّهَا ٱلضَّآلُّونَ ٱلۡمُكَذِّبُونَ
"Sa'an nan lalle ku, ya kũ ɓatattu, mãsu ƙaryatãwa!"
Aya :
52
لَأٓكِلُونَ مِن شَجَرٖ مِّن زَقُّومٖ
"Lalle mãsu cĩ ne daga wata itãciya ta zaƙƙum (ɗanyen wutã)."
Aya :
53
فَمَالِـُٔونَ مِنۡهَا ٱلۡبُطُونَ
"Har za ku zama mãsu cika cikunna daga gare ta."
Aya :
54
فَشَٰرِبُونَ عَلَيۡهِ مِنَ ٱلۡحَمِيمِ
"Sa'an nan kuma mãsu shã ne, a kan wannan abin cin, daga ruwan zãfi."
Aya :
55
فَشَٰرِبُونَ شُرۡبَ ٱلۡهِيمِ
"Ku zama mãsu shã irin shan rãƙuma mãsu ƙishirwa."
Aya :
56
هَٰذَا نُزُلُهُمۡ يَوۡمَ ٱلدِّينِ
Wannan ita ce liyãfarsu a rãnar sakamako.
Aya :
57
نَحۡنُ خَلَقۡنَٰكُمۡ فَلَوۡلَا تُصَدِّقُونَ
Mũ ne Muka halitta ku, to, don me bã zã ku gaskata ba?
Aya :
58
أَفَرَءَيۡتُم مَّا تُمۡنُونَ
Shin kuma kun ga abin da kuke fitarwa na maniyyi?
Aya :
59
ءَأَنتُمۡ تَخۡلُقُونَهُۥٓ أَمۡ نَحۡنُ ٱلۡخَٰلِقُونَ
Shin kũ ne kuke halitta shi, kõ kuwa mũ ne Mãsu halittãwa?
Aya :
60
نَحۡنُ قَدَّرۡنَا بَيۡنَكُمُ ٱلۡمَوۡتَ وَمَا نَحۡنُ بِمَسۡبُوقِينَ
Mũ ne Muka ƙaddara mutuwa a tsakãninku, kuma ba Mu zama Mãsu gajiyãwa* ba,
Aya :
61
عَلَىٰٓ أَن نُّبَدِّلَ أَمۡثَٰلَكُمۡ وَنُنشِئَكُمۡ فِي مَا لَا تَعۡلَمُونَ
A kan Mu musanya waɗansu (mutãne) kamarku, kuma Mu mayar da ku a cikin wata halitta da ba ku sani ba.
Aya :
62
وَلَقَدۡ عَلِمۡتُمُ ٱلنَّشۡأَةَ ٱلۡأُولَىٰ فَلَوۡلَا تَذَكَّرُونَ
Kuma lalle, ne haƙĩƙa, kun san halittar farko, to, don me ba zã ku yi tunãni ba?
Aya :
63
أَفَرَءَيۡتُم مَّا تَحۡرُثُونَ
Shin, kuma kun ga abin da kũke nõmãwa?
Aya :
64
ءَأَنتُمۡ تَزۡرَعُونَهُۥٓ أَمۡ نَحۡنُ ٱلزَّٰرِعُونَ
Shin, kũ ne ke tsirar da shi kõ kuwa Mũ ne Mãsu tsirarwa?
Aya :
65
لَوۡ نَشَآءُ لَجَعَلۡنَٰهُ حُطَٰمٗا فَظَلۡتُمۡ تَفَكَّهُونَ
Dã Munã so lalle, da Mun sanya shi bũsasshiyar ciyãwa, sai ku yini kunã mãmãkin bãƙin ciki.
Aya :
66
إِنَّا لَمُغۡرَمُونَ
(Kunã cẽwa) "Lalle haƙĩƙa an azã mana tãra!"
Aya :
67
بَلۡ نَحۡنُ مَحۡرُومُونَ
"Ã'a, mun dai zama waɗanda aka hanã wa!"
Aya :
68
أَفَرَءَيۡتُمُ ٱلۡمَآءَ ٱلَّذِي تَشۡرَبُونَ
Shin, kuma kun ga ruwa wannan da kuke sha?
Aya :
69
ءَأَنتُمۡ أَنزَلۡتُمُوهُ مِنَ ٱلۡمُزۡنِ أَمۡ نَحۡنُ ٱلۡمُنزِلُونَ
Shin, kũ ne kuke saukar da shi daga girgije, kõ kuwa Mũne Mãsu saukarwa?
Aya :
70
لَوۡ نَشَآءُ جَعَلۡنَٰهُ أُجَاجٗا فَلَوۡلَا تَشۡكُرُونَ
Dã Mun so, dã Mun mayar da shi ruwan zartsi. To don me bã ku gõdẽwa?
Aya :
71
أَفَرَءَيۡتُمُ ٱلنَّارَ ٱلَّتِي تُورُونَ
Shin, kuma kun ga wutã wannan da kuke ƙyastãwa?
Aya :
72
ءَأَنتُمۡ أَنشَأۡتُمۡ شَجَرَتَهَآ أَمۡ نَحۡنُ ٱلۡمُنشِـُٔونَ
Shin, kũ ne kuke ƙagã halittar itãciyarta, kõ kuwa Mũ ne Mãsu ƙãgãwa?
Aya :
73
نَحۡنُ جَعَلۡنَٰهَا تَذۡكِرَةٗ وَمَتَٰعٗا لِّلۡمُقۡوِينَ
Mũ ne Muka sanya ta wata abar wa'azi da jin dãɗi ga matafiya a cikin jẽji.
Aya :
74
فَسَبِّحۡ بِٱسۡمِ رَبِّكَ ٱلۡعَظِيمِ
Sai ka tsarkake sũnan Ubangijinka Mai girma.
Aya :
75
۞ فَلَآ أُقۡسِمُ بِمَوَٰقِعِ ٱلنُّجُومِ
To, bã sai Na yi rantsuwa ba da lõkutan fãɗuwar taurãri.
Aya :
76
وَإِنَّهُۥ لَقَسَمٞ لَّوۡ تَعۡلَمُونَ عَظِيمٌ
Kuma lalle ne' haƙĩƙa, rantsuwa ce mai girma, dã kun sani.