Aya :
11
يُبَصَّرُونَهُمۡۚ يَوَدُّ ٱلۡمُجۡرِمُ لَوۡ يَفۡتَدِي مِنۡ عَذَابِ يَوۡمِئِذِۭ بِبَنِيهِ
Ana sanya su, su gajũna, mai laifi na gũrin dã zai iya yin fansa, daga azãbar rãnar nan, da ɗiyansa,
Aya :
12
وَصَٰحِبَتِهِۦ وَأَخِيهِ
Da matarsa da ɗan'uwansa.
Aya :
13
وَفَصِيلَتِهِ ٱلَّتِي تُـٔۡوِيهِ
Da danginsa, mãsu tattarã shi.
Aya :
14
وَمَن فِي ٱلۡأَرۡضِ جَمِيعٗا ثُمَّ يُنجِيهِ
Da wanda ke a cikin dũniya duka gabã ɗaya, sa'an nan fansar, ta tsĩrar da shi.
Aya :
15
كَلَّآۖ إِنَّهَا لَظَىٰ
A'aha! Lalle ne fa, ita ce Lazã,
Aya :
16
نَزَّاعَةٗ لِّلشَّوَىٰ
Mai twãle fãtar goshi.
Aya :
17
تَدۡعُواْ مَنۡ أَدۡبَرَ وَتَوَلَّىٰ
Tanã kiran wanda ya jũya bãya (daga addini) kuma ya kau da kai.
Aya :
18
وَجَمَعَ فَأَوۡعَىٰٓ
Ya tãra (dũkiya), kuma ya sanya ta a cikin jaka.
Aya :
19
۞ إِنَّ ٱلۡإِنسَٰنَ خُلِقَ هَلُوعًا
Lalle ne mutum an halitta shi mai ciwon kwaɗayi.
Aya :
20
إِذَا مَسَّهُ ٱلشَّرُّ جَزُوعٗا
Idan sharri ya shãfe shi, ya kãsa haƙuri.
Aya :
21
وَإِذَا مَسَّهُ ٱلۡخَيۡرُ مَنُوعًا
Kuma idan alhẽri ya shãfe shi, ya yi rõwa.
Aya :
22
إِلَّا ٱلۡمُصَلِّينَ
Sai mãsu yin salla,
Aya :
23
ٱلَّذِينَ هُمۡ عَلَىٰ صَلَاتِهِمۡ دَآئِمُونَ
Waɗanda suke, a kan sallarsu, su, mãsu dawwama ne.
Aya :
24
وَٱلَّذِينَ فِيٓ أَمۡوَٰلِهِمۡ حَقّٞ مَّعۡلُومٞ
Kuma waɗanda a cikin dũkiyarsu, akwai wani haƙƙi sananne.
Aya :
25
لِّلسَّآئِلِ وَٱلۡمَحۡرُومِ
Ga (matalauci) mai rõƙo da wanda aka hanã wa roƙon.
Aya :
26
وَٱلَّذِينَ يُصَدِّقُونَ بِيَوۡمِ ٱلدِّينِ
Da waɗannan da ke gaskata rãnar sakamako.
Aya :
27
وَٱلَّذِينَ هُم مِّنۡ عَذَابِ رَبِّهِم مُّشۡفِقُونَ
Da waɗannan sabõda azãbar Ubangijinsu, suna jin tsõro.
Aya :
28
إِنَّ عَذَابَ رَبِّهِمۡ غَيۡرُ مَأۡمُونٖ
Lalle ne, azãbar Ubangijinsu bã wadda ake iya amincẽwaba ce.
Aya :
29
وَٱلَّذِينَ هُمۡ لِفُرُوجِهِمۡ حَٰفِظُونَ
Da waɗanda suke, ga farjojinsu, mãsu tsarewa ne.
Aya :
30
إِلَّا عَلَىٰٓ أَزۡوَٰجِهِمۡ أَوۡ مَا مَلَكَتۡ أَيۡمَٰنُهُمۡ فَإِنَّهُمۡ غَيۡرُ مَلُومِينَ
Sai fa a kan matan aurensu da abin da hannayensu na dãma suka mallaka. To lalle ne sũkam ba waɗanda ake zargi ba ne.
Aya :
31
فَمَنِ ٱبۡتَغَىٰ وَرَآءَ ذَٰلِكَ فَأُوْلَٰٓئِكَ هُمُ ٱلۡعَادُونَ
To, duk wanda ya nẽmi abin da yake a bayan wannan, to, waɗancan sũ ne mãsu ƙetare iyãka.
Aya :
32
وَٱلَّذِينَ هُمۡ لِأَمَٰنَٰتِهِمۡ وَعَهۡدِهِمۡ رَٰعُونَ
Kuma da waɗannan da suke ga amãnõninsu da alkawarinsu mãsu tsarẽwa ne.
Aya :
33
وَٱلَّذِينَ هُم بِشَهَٰدَٰتِهِمۡ قَآئِمُونَ
Kuma da waɗanda suke, ga shaidarsu, mãsu dãgẽwa ne.
Aya :
34
وَٱلَّذِينَ هُمۡ عَلَىٰ صَلَاتِهِمۡ يُحَافِظُونَ
Kuma waɗanda suke, a kan sallarsu, mãsu tsarẽwa ne.
Aya :
35
أُوْلَٰٓئِكَ فِي جَنَّٰتٖ مُّكۡرَمُونَ
Waɗannan, a cikin gidãjen Aljanna, waɗanda ake girmamãwa ne
Aya :
36
فَمَالِ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ قِبَلَكَ مُهۡطِعِينَ
Mẽ yã sãmi waɗanda suka kãfirta, a wajenka, sunã gaugãwar (gudu).
Aya :
37
عَنِ ٱلۡيَمِينِ وَعَنِ ٱلشِّمَالِ عِزِينَ
Daga jihar dãma, kuma daga jihar hagu, jama'a-jama'a!
Aya :
38
أَيَطۡمَعُ كُلُّ ٱمۡرِيٕٖ مِّنۡهُمۡ أَن يُدۡخَلَ جَنَّةَ نَعِيمٖ
Shin kõwane mutum daga cikinsu yana nẽman a shigar da shi a Aljannar ni'ima ne (ba da wani aiki ba)?
Aya :
39
كَلَّآۖ إِنَّا خَلَقۡنَٰهُم مِّمَّا يَعۡلَمُونَ
A'aha! Lalle Mũ, Mun halitta su, daga abin da suka sani.