Aya :
7
كَلَّآ إِنَّ كِتَٰبَ ٱلۡفُجَّارِ لَفِي سِجِّينٖ
Haƙĩƙa lalle ne littãfin fãjirai dãhir, yana a cikin Sijjĩn.
Aya :
8
وَمَآ أَدۡرَىٰكَ مَا سِجِّينٞ
Kuma, mẽ ya sanar da kai abin da akẽ cẽ wa Sijjĩn?
Aya :
9
كِتَٰبٞ مَّرۡقُومٞ
Wani ittãfi ne rubũtacce.
Aya :
10
وَيۡلٞ يَوۡمَئِذٖ لِّلۡمُكَذِّبِينَ
Bone yã tabbata a rãnar nan ga mãsu ƙaryatãwa.
Aya :
11
ٱلَّذِينَ يُكَذِّبُونَ بِيَوۡمِ ٱلدِّينِ
Waɗanda suke ƙaryatãwa game da rãnar sakamako.
Aya :
12
وَمَا يُكَذِّبُ بِهِۦٓ إِلَّا كُلُّ مُعۡتَدٍ أَثِيمٍ
Babũ mai ƙaryatãwa gare shi fãce dukan mai ƙẽtare haddi mai yawan zunubi.
Aya :
13
إِذَا تُتۡلَىٰ عَلَيۡهِ ءَايَٰتُنَا قَالَ أَسَٰطِيرُ ٱلۡأَوَّلِينَ
Idan ana karãtun ãyõyinmu, a kansa, sai ya ce: tãtsũniyõyin mutãnen farko ne.
Aya :
14
كَلَّاۖ بَلۡۜ رَانَ عَلَىٰ قُلُوبِهِم مَّا كَانُواْ يَكۡسِبُونَ
A'aha! Bã haka ba, abin da suka kasance suna aikatãwa dai, yã yi tsãtsa a cikin zukãtãnsu.
Aya :
15
كَلَّآ إِنَّهُمۡ عَن رَّبِّهِمۡ يَوۡمَئِذٖ لَّمَحۡجُوبُونَ
A'aha! Haƙĩƙa, lalle ne sũ daga Ubangijinsu, rãnar nan, waɗanda ake shãmakancẽwa ne.
Aya :
16
ثُمَّ إِنَّهُمۡ لَصَالُواْ ٱلۡجَحِيمِ
Sa'an nan, lalle ne, sũ mãsu shiga cikin Jahĩm ne.
Aya :
17
ثُمَّ يُقَالُ هَٰذَا ٱلَّذِي كُنتُم بِهِۦ تُكَذِّبُونَ
Sa'an nan a ce: "Wannan shi ne abin da kuka kasance kuna ƙaryatãwa game da shi."
Aya :
18
كَلَّآ إِنَّ كِتَٰبَ ٱلۡأَبۡرَارِ لَفِي عِلِّيِّينَ
A'aha! Haƙĩƙa lalle ne littãfin mãsu ɗã'ã yana a cikin Illiyyĩna?
Aya :
19
وَمَآ أَدۡرَىٰكَ مَا عِلِّيُّونَ
Kuma mẽne ne yã sanar da kai abin da ake cẽwa Illiyyũna?
Aya :
20
كِتَٰبٞ مَّرۡقُومٞ
Wani littãfi ne rubũtacce.
Aya :
21
يَشۡهَدُهُ ٱلۡمُقَرَّبُونَ
Muƙarrabai* suke halarta shi.
Aya :
22
إِنَّ ٱلۡأَبۡرَارَ لَفِي نَعِيمٍ
Lalle ne, mãsu ɗã'ã ga Allah tabbas suna cikin ni'ima.
Aya :
23
عَلَى ٱلۡأَرَآئِكِ يَنظُرُونَ
A kan karagu, suna ta kallo.
Aya :
24
تَعۡرِفُ فِي وُجُوهِهِمۡ نَضۡرَةَ ٱلنَّعِيمِ
Kana sani a cikin fuskõkinsu, akwai kwarjinin ni'ima.
Aya :
25
يُسۡقَوۡنَ مِن رَّحِيقٖ مَّخۡتُومٍ
Ana shãyar da sũ daga wata giya wadda aka yunƙe a kan rufinta.
Aya :
26
خِتَٰمُهُۥ مِسۡكٞۚ وَفِي ذَٰلِكَ فَلۡيَتَنَافَسِ ٱلۡمُتَنَٰفِسُونَ
¡arshen kurɓinta miski ne. To, a cikin wannan, mãsu gwagwarmaya su yi ta gwagwarmayar nẽma.
Aya :
27
وَمِزَاجُهُۥ مِن تَسۡنِيمٍ
Kuma abin da ake gauraya ta da shi, daga tasnĩm yake.
Aya :
28
عَيۡنٗا يَشۡرَبُ بِهَا ٱلۡمُقَرَّبُونَ
(Wato) wani marmaro ne wanda muƙarrabai ke sha daga gare shi.
Aya :
29
إِنَّ ٱلَّذِينَ أَجۡرَمُواْ كَانُواْ مِنَ ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ يَضۡحَكُونَ
Lalle ne, waɗanda suka kãfirta sun kasance (a dũniya) suna yi wa waɗanda suka yi ĩmãni dãriya.
Aya :
30
وَإِذَا مَرُّواْ بِهِمۡ يَتَغَامَزُونَ
Kuma idan sun shuɗe su sai su dinga yin zunɗe.
Aya :
31
وَإِذَا ٱنقَلَبُوٓاْ إِلَىٰٓ أَهۡلِهِمُ ٱنقَلَبُواْ فَكِهِينَ
Kuma idan suka jũya zuwa ga iyãlansu, sai su tafi suna kãkãci.
Aya :
32
وَإِذَا رَأَوۡهُمۡ قَالُوٓاْ إِنَّ هَٰٓؤُلَآءِ لَضَآلُّونَ
Kuma idan sun gan su sai su ce: "Lalle waɗannan ɓatattu ne."
Aya :
33
وَمَآ أُرۡسِلُواْ عَلَيۡهِمۡ حَٰفِظِينَ
Alhãli kuwa, ba a aike su ba dõmin su zama mãsu tsaro a kansu.
Aya :
34
فَٱلۡيَوۡمَ ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ مِنَ ٱلۡكُفَّارِ يَضۡحَكُونَ
To, yau fa (a Lãhira] waɗanda suka yi ĩmãni, sũ ke yi wa kãfirai dãriya.