Aya :
1
ٱقۡرَأۡ بِٱسۡمِ رَبِّكَ ٱلَّذِي خَلَقَ
Ka yi karatu da sunan Ubangijinka, wanda Ya yi halitta.
Aya :
2
خَلَقَ ٱلۡإِنسَٰنَ مِنۡ عَلَقٍ
Ya hahitta mutum daga gudan jini.
Aya :
3
ٱقۡرَأۡ وَرَبُّكَ ٱلۡأَكۡرَمُ
Ka yi karatu, kuma Ubangijinka shi ne Mafi karimci.
Aya :
4
ٱلَّذِي عَلَّمَ بِٱلۡقَلَمِ
Wanda Ya sanar (da mutum) game da alƙalami.
Aya :
5
عَلَّمَ ٱلۡإِنسَٰنَ مَا لَمۡ يَعۡلَمۡ
Ya sanar da mutum abin da bai sani ba.
Aya :
6
كَلَّآ إِنَّ ٱلۡإِنسَٰنَ لَيَطۡغَىٰٓ
A'aha! Lalle, ne mutum haƙĩƙa, yana girman kai (ya ƙi karatu).
Aya :
7
أَن رَّءَاهُ ٱسۡتَغۡنَىٰٓ
Dõmin yã ga kansa, yã wadãta.
Aya :
8
إِنَّ إِلَىٰ رَبِّكَ ٱلرُّجۡعَىٰٓ
Lalle ne zuwa ga Ubangijinka makoma take.
Aya :
9
أَرَءَيۡتَ ٱلَّذِي يَنۡهَىٰ
Shin, kã ga wanda ke hana.
Aya :
10
عَبۡدًا إِذَا صَلَّىٰٓ
Bãwã idan yã yi salla?
Aya :
11
أَرَءَيۡتَ إِن كَانَ عَلَى ٱلۡهُدَىٰٓ
Ashe, kã gani, idan (shi bãwan) ya kasance a kan shiriya?
Aya :
12
أَوۡ أَمَرَ بِٱلتَّقۡوَىٰٓ
Ko ya yi umurni da taƙawa?
Aya :
13
أَرَءَيۡتَ إِن كَذَّبَ وَتَوَلَّىٰٓ
Ashe, kã gani, idan (shi mai hanin) ya ƙaryata, kuma ya jũya bãya?
Aya :
14
أَلَمۡ يَعۡلَم بِأَنَّ ٱللَّهَ يَرَىٰ
Ashe, bai sani ba cewa Allah Yanã gani?
Aya :
15
كَلَّا لَئِن لَّمۡ يَنتَهِ لَنَسۡفَعَۢا بِٱلنَّاصِيَةِ
A'aha! Lalle ne, idan bai hanu ba, lalle ne zã Mu ja gãshin makwarkwaɗa.
Aya :
16
نَاصِيَةٖ كَٰذِبَةٍ خَاطِئَةٖ
Makwarkwaɗa maƙaryaciya, mai laifi.
Aya :
17
فَلۡيَدۡعُ نَادِيَهُۥ
Sai ya kirayi ƙungiyarsa.
Aya :
18
سَنَدۡعُ ٱلزَّبَانِيَةَ
Zã Mu kirayi zabaniyãwa (mala'iku mãsu girma).
Aya :
19
كَلَّا لَا تُطِعۡهُ وَٱسۡجُدۡۤ وَٱقۡتَرِب۩
A'aha kada ka bĩ shi. Kuma ka yi tawali'u,* kuma ka nemi kusanta (zuwa ga Ubangijinka).