Aya :
1
وَٱلَّيۡلِ إِذَا يَغۡشَىٰ
Inã rantsuwa da dare a lõkacin da yake rufẽwa.
Aya :
2
وَٱلنَّهَارِ إِذَا تَجَلَّىٰ
Da yini a lõkacin da yake kuranyẽwa.
Aya :
3
وَمَا خَلَقَ ٱلذَّكَرَ وَٱلۡأُنثَىٰٓ
Da abin da ya halitta namiji da mace.
Aya :
4
إِنَّ سَعۡيَكُمۡ لَشَتَّىٰ
Lãlle ne ayyukanku, dabam-dabam suke.
Aya :
5
فَأَمَّا مَنۡ أَعۡطَىٰ وَٱتَّقَىٰ
To, amma wanda ya yi kyauta, kuma ya yi taƙawa.
Aya :
6
وَصَدَّقَ بِٱلۡحُسۡنَىٰ
Kuma ya gaskata kalma* mai kyãwo.
Aya :
7
فَسَنُيَسِّرُهُۥ لِلۡيُسۡرَىٰ
To, zã Mu sauƙaƙe masa har ya kai ga sauƙi.
Aya :
8
وَأَمَّا مَنۢ بَخِلَ وَٱسۡتَغۡنَىٰ
Kuma amma wanda ya yi rõwa, kuma ya wadãtu da kansa.
Aya :
9
وَكَذَّبَ بِٱلۡحُسۡنَىٰ
Kuma ya ƙaryatar da kalma mai kyãwo.
Aya :
10
فَسَنُيَسِّرُهُۥ لِلۡعُسۡرَىٰ
To, zã Mu sauƙaƙke masa har ya kai ga tsanani.
Aya :
11
وَمَا يُغۡنِي عَنۡهُ مَالُهُۥٓ إِذَا تَرَدَّىٰٓ
Kuma dũkiyarsa ba ta wadãtar masa da kõme ba, a lõkacin da ya gangara (a wuta).
Aya :
12
إِنَّ عَلَيۡنَا لَلۡهُدَىٰ
Lãlle aikin Mu ne, Mu bayyana shiriya.
Aya :
13
وَإِنَّ لَنَا لَلۡأٓخِرَةَ وَٱلۡأُولَىٰ
Kuma lalle ne Lãhira da duniya Namu ne.
Aya :
14
فَأَنذَرۡتُكُمۡ نَارٗا تَلَظَّىٰ
Sabõda haka, Na yi maku gargaɗi da wuta mai babbaka.